< Mattiyu 6 >
1 “Ku yi hankali kada ku nuna ‘ayyukanku na adalci’ a gaban mutane, don su gani. In kuka yi haka, ba za ku sami lada daga wurin Ubanku da yake cikin sama ba.
„Ära tee oma häid tegusid inimeste ees, lihtsalt selleks, et neid näha oleks. Muidu ei saa sa mingit tasu Isalt, kes on taevas.
2 “Saboda haka sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yi shelarsa, yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan tituna, don mutane su yabe su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
Kui sa vaestele annad, ära ole nagu silmakirjatsejad, kes puhuvad pasunaid, et teada anda, mida nad teevad sünagoogides ja tänavatel, nii et inimesed ülistaksid neid. Ma ütlen teile tõde: nad on oma tasu juba kätte saanud.
3 Amma sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yarda hannun hagunka yă ma san abin da hannun damarka yake yi,
Kui sa annad vaestele, siis ärgu sinu vasak käsi teadku, mida su parem käsi teeb.
4 don bayarwarka ta zama a ɓoye. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
Nii on see, mida sa annad, salajane, ja su Isa, kes näeb, mis toimub salajas, tasub sulle.
5 “Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku zama kamar munafukai, gama sun cika son yin addu’a a tsaye a cikin majami’u da kuma a bakin titi, don mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
Kui sa palvetad, siis ära ole nagu silmakirjatsejad, sest neile meeldib püsti tõusta ja palvetada sünagoogides ja tänavanurkadel, nii et inimesed neid näeksid. Ma luban teile, nad on oma tasu juba kätte saanud.
6 Amma sa’ad da kake addu’a, sai ka shiga ɗakinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanka wanda ba a gani. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
Aga sina, kui sa palvetad, mine tuppa ja sulge uks ning palveta oma Isa poole salajas, ja su Isa, kes näeb, mis toimub salajas, tasub sulle.
7 Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku yi ta maimaita magana, kamar marasa sanin Allah, domin suna tsammani za a ji su saboda yawan maganarsu.
Kui sa palvetad, siis ära lobise mõttetult nagu võõrad, kes arvavad, et neid kuuldakse kõigi nende sõnade pärast, mida nad kordavad.
8 Kada ku zama kamar su, gama Ubanku ya san abin da kuke bukata kafin ma ku roƙe shi.
Ärge olge nende moodi, sest teie Isa teab, mida te vajate juba enne, kui te temalt palute.
9 “To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a. “‘Ubanmu wanda yake cikin sama, a tsarkake sunanka,
Palvetage siis nõnda: „Meie taevane Isa, austatud olgu sinu nimi.
10 mulkinka yă zo a aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a sama.
Sinu riik tulgu! Sinu tahe täitugu maa peal samamoodi nagu taevas.
11 Ka ba mu yau abincin yininmu.
Palun anna meile täna toitu, mida vajame.
12 Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.
Andesta meie patud, nagu meie oleme andestanud neile, kes on meie vastu pattu teinud.
13 Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
Palun ära lase meil kiusatusele järele anda ja päästa meid kurja käest.“
14 Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku.
Sest kui te annate andeks neile, kes teie vastu patustavad, annab ka teie taevane Isa teile andeks.
15 Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.
Aga kui te ei anna andeks neile, kes teie vastu patustavad, siis ei anna teie taevane Isa teie patte andeks.
16 “Sa’ad da kuma kuna azumi, kada ku ɓata fuska, yadda munafukai suke yi. Sukan ɓata fuskokinsu domin su nuna wa mutane cewa suna azumi. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
Kui sa paastud, siis ära ole nagu silmakirjatsejad, kes teevad kurva näo ja jätavad oma välimuse hooletusse, et kõik näeksid, et nad paastuvad. Ma ütlen teile tõde: nad on oma tasu juba kätte saanud.
17 Amma sa’ad da kana azumi, ka shafa wa kanka mai, ka wanke fuskarka,
Aga kui sina paastud, pese oma nägu ja tee välimus korda,
18 domin kada mutane su ga alama cewa kana azumi, sai dai Ubanka kaɗai wanda ba a gani; Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
et inimesed ei näeks, et sa paastud, ning su nähtamatu Isa, kes näeb, mis toimub salajas, tasub sulle.
19 “Kada ku yi wa kanku ajiyar dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda kuma ɓarayi sukan fasa, su yi sata.
Ärge kuhjake rikkust siia maa peale, kus koi ja rooste seda rikuvad ning kus vargad sisse murravad ja selle varastavad.
20 Amma ku yi wa kanku ajiyar dukiya a sama, inda ba tsatsa da asu da za su ɓata su, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa, su yi sata.
Selle asemel koguge oma vara taevasse, kus koid ja rooste seda ei riku ning kus vargad sisse ei murra ega seda varasta.
21 Gama inda dukiyarka take, a nan ne fa zuciyarka za tă kasance.
Sest see, mida sa kõige enam hindad, näitab, kes sa tegelikult oled.
22 “Ido shi ne fitilar jiki. In idanunka suna da kyau, dukan jikinka zai cika da haske.
Silm on nagu lamp, mis valgustab ihu. Niisiis, kui su silm on terve, siis on kogu su ihul valgus.
23 Amma in idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma zai cika da duhu. To, in hasken da yake a cikinka duhu ne, duhun ya wuce misali ke nan!
Aga kui su silm on kuri, on kogu su ihu pimeduses. Kui „valgus“, mis sul on, on tegelikult pimedus, kui pime see siis on!
24 “Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu. Ko dai yă ƙi ɗaya, yă ƙaunaci ɗaya, ko kuwa yă yi aminci ga ɗaya, sa’an nan yă rena ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah, ku kuma bauta wa kuɗi gaba ɗaya.”
Keegi ei saa teenida kaht isandat. Sa kas vihkad üht ja armastad teist või oled pühendunud ühele ja põlgad teist. Te ei saa teenida Jumalat ja Raha.
25 “Saboda haka, ina gaya muku, kada ku damu game da rayuwarku, game da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha; ko kuma game da jikinku, game da abin da za ku sa. Ashe, rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
Sellepärast ma ütlengi teile, et ärge muretsege oma elu pärast. Ärge muretsege sellepärast, mida süüa või mida juua või missugused rõivad selga panna. Kas elu ei ole olulisem kui toit ja ihu olulisem kui rõivad?
26 Ku dubi tsuntsayen sararin sama mana; ba sa shuki ko girbi ko ajiya a rumbuna, duk da haka, Ubanku na sama yana ciyar da su. Ashe, ba ku fi su daraja nesa ba?
Pange tähele linde − nad ei külva ega lõika ega hoia toidust aitades, sest teie taevane Isa toidab neid. Kas teie ei ole rohkem väärt kui nemad?
27 Wane ne a cikinku ta wurin damuwa zai iya ƙara wa rayuwarsa ko sa’a ɗaya?
Kes teist suudaks muretsemisega oma elule minutigi lisada?
28 “Me ya sa kuke damuwa a kan riguna? Ku dubi yadda furannin jeji suke girma mana. Ba sa aiki ko saƙa.
Ja miks te muretsete rõivaste pärast? Vaadake kauneid lilli väljal. Vaadake, kuidas nad kasvavad: nad ei tee rasket tööd, nad ei ketra lõnga.
29 Duk da haka ina gaya muku ko Solomon cikin dukan darajarsa bai sa kayan adon da ya kai na ko ɗaya a cikinsu ba.
Aga ma ütlen teile, isegi Saalomon kogu oma hiilguses ei olnud riietatud nii, nagu üks neist lilledest.
30 In haka Allah yake yi wa ciyawar jeji sutura, wadda yau tana nan, gobe kuwa a jefa a cikin wuta, ba zai ma fi yi muku sutura ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?
Niisiis, kui Jumal ehib sedasi väljal heina, mis täna on ja homme visatakse tulle, kas ta siis ei tee palju enam teie heaks, te inimesed, kes nii vähe usaldavad?
31 Don haka, kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci?’ Ko, ‘Me za mu sha?’ Ko kuma, ‘Me za mu sa?’
Ärge siis muretsege, öeldes: „Mida me sööme?“või „Mida me joome?“või „Mida me selga paneme?“
32 Gama marasa sanin Allah suna fama neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
Kõiki neid asju taotlevad paganad, aga teie taevane Isa teab kõike, mida teil vaja on.
33 Da farko dai, ku nemi mulkin Allah da kuma adalcinsa, za a kuwa ba ku dukan waɗannan abubuwa.
Taotlege kõigepealt tema riiki ja õiget eluviisi ning teile antakse kõike.
34 Saboda haka kada ku damu game da gobe, gama gobe zai damu da kansa. Damuwar yau ma ta isa wahala.
Seega ärge muretsege homse pärast, sest homne päev suudab ise enda eest muretseda. Igas päevas on juba piisavalt halba.“