< Mattiyu 6 >

1 “Ku yi hankali kada ku nuna ‘ayyukanku na adalci’ a gaban mutane, don su gani. In kuka yi haka, ba za ku sami lada daga wurin Ubanku da yake cikin sama ba.
Takith hede, that ye do not youre riytwisnesse bifor men, to be seyn of hem, ellis ye schulen haue no meede at youre fadir that is in heuenes.
2 “Saboda haka sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yi shelarsa, yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan tituna, don mutane su yabe su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
Therfore whanne thou doist almes, nyle thou trumpe tofore thee, as ypocritis doon in synagogis and stretis, that thei be worschipid of men; sotheli Y seie to you, they han resseyued her meede.
3 Amma sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yarda hannun hagunka yă ma san abin da hannun damarka yake yi,
But whanne thou doist almes, knowe not thi left hond what thi riyt hond doith, that thin almes be in hidils,
4 don bayarwarka ta zama a ɓoye. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
and thi fadir that seeth in hiddils, schal quyte thee.
5 “Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku zama kamar munafukai, gama sun cika son yin addu’a a tsaye a cikin majami’u da kuma a bakin titi, don mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
And whanne ye preyen, ye schulen not be as ipocritis, that louen to preye stondynge in synagogis and corneris of stretis, to be seyn of men; treuli Y seie to you, thei han resseyued her meede.
6 Amma sa’ad da kake addu’a, sai ka shiga ɗakinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanka wanda ba a gani. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
But whanne thou schalt preye, entre in to thi couche, and whanne the dore is schet, preye thi fadir in hidils, and thi fadir that seeth in hidils, schal yelde to thee.
7 Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku yi ta maimaita magana, kamar marasa sanin Allah, domin suna tsammani za a ji su saboda yawan maganarsu.
But in preiyng nyle yee speke myche, as hethene men doon, for thei gessen that thei ben herd in her myche speche.
8 Kada ku zama kamar su, gama Ubanku ya san abin da kuke bukata kafin ma ku roƙe shi.
Therfor nyle ye be maad lich to hem, for your fadir woot what is nede to you, bifore that ye axen hym.
9 “To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a. “‘Ubanmu wanda yake cikin sama, a tsarkake sunanka,
And thus ye schulen preye, Oure fadir that art in heuenes, halewid be thi name;
10 mulkinka yă zo a aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a sama.
thi kyngdoom come to; be thi wille don `in erthe as in heuene;
11 Ka ba mu yau abincin yininmu.
yyue to vs this dai oure `breed ouer othir substaunce;
12 Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.
and foryyue to vs oure dettis, as we foryyuen to oure dettouris;
13 Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
and lede vs not in to temptacioun, but delyuere vs fro yuel. Amen.
14 Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku.
For if ye foryyuen to men her synnes, youre heuenli fadir schal foryyue to you youre trespassis.
15 Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.
Sotheli if ye foryyuen not to men, nether youre fadir schal foryyue to you youre synnes.
16 “Sa’ad da kuma kuna azumi, kada ku ɓata fuska, yadda munafukai suke yi. Sukan ɓata fuskokinsu domin su nuna wa mutane cewa suna azumi. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
But whanne ye fasten, nyle ye be maad as ypocritis sorewful, for thei defacen hem silf, to seme fastyng to men; treuli Y seie to you, they han resseyued her meede.
17 Amma sa’ad da kana azumi, ka shafa wa kanka mai, ka wanke fuskarka,
But whanne thou fastist, anoynte thin heed, and waische thi face,
18 domin kada mutane su ga alama cewa kana azumi, sai dai Ubanka kaɗai wanda ba a gani; Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
that thou be not seen fastynge to men, but to thi fadir that is in hidlis, and thi fadir that seeth in priuey, shal yelde to thee.
19 “Kada ku yi wa kanku ajiyar dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda kuma ɓarayi sukan fasa, su yi sata.
Nile ye tresoure to you tresouris in erthe, where ruste and mouyte destrieth, and where theues deluen out and stelen;
20 Amma ku yi wa kanku ajiyar dukiya a sama, inda ba tsatsa da asu da za su ɓata su, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa, su yi sata.
but gadere to you tresouris in heuene, where nether ruste ne mouyte distrieth, and where theues deluen not out, ne stelen.
21 Gama inda dukiyarka take, a nan ne fa zuciyarka za tă kasance.
For where thi tresoure is, there also thin herte is.
22 “Ido shi ne fitilar jiki. In idanunka suna da kyau, dukan jikinka zai cika da haske.
The lanterne of thi bodi is thin iye; if thin iye be symple, al thi bodi shal be liytful;
23 Amma in idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma zai cika da duhu. To, in hasken da yake a cikinka duhu ne, duhun ya wuce misali ke nan!
but if thin iye be weiward, al thi bodi shal be derk. If thanne the liyt that is in thee be derknessis, how grete schulen thilk derknessis be?
24 “Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu. Ko dai yă ƙi ɗaya, yă ƙaunaci ɗaya, ko kuwa yă yi aminci ga ɗaya, sa’an nan yă rena ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah, ku kuma bauta wa kuɗi gaba ɗaya.”
No man may serue tweyn lordis, for ethir he schal hate `the toon, and loue the tother; ethir he shal susteyne `the toon, and dispise the tothir. Ye moun not serue God and richessis.
25 “Saboda haka, ina gaya muku, kada ku damu game da rayuwarku, game da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha; ko kuma game da jikinku, game da abin da za ku sa. Ashe, rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
Therfor I seie to you, that ye be not bisi to youre lijf, what ye schulen ete; nether to youre bodi, with what ye schulen be clothid. Whether lijf is not more than meete, and the bodie more than cloth?
26 Ku dubi tsuntsayen sararin sama mana; ba sa shuki ko girbi ko ajiya a rumbuna, duk da haka, Ubanku na sama yana ciyar da su. Ashe, ba ku fi su daraja nesa ba?
Biholde ye the foulis of the eire, for thei sowen not, nethir repen, nethir gaderen in to bernes; and youre fadir of heuene fedith hem. Whether ye ben not more worthi than thei?
27 Wane ne a cikinku ta wurin damuwa zai iya ƙara wa rayuwarsa ko sa’a ɗaya?
But who of you thenkynge mai putte to his stature o cubit?
28 “Me ya sa kuke damuwa a kan riguna? Ku dubi yadda furannin jeji suke girma mana. Ba sa aiki ko saƙa.
And of clothing what ben ye bisye? Biholde ye the lilies of the feeld, how thei wexen. Thei trauelen not, nether spynnen;
29 Duk da haka ina gaya muku ko Solomon cikin dukan darajarsa bai sa kayan adon da ya kai na ko ɗaya a cikinsu ba.
and Y seie to you, Salomon in al his glorie was not keuered as oon of these.
30 In haka Allah yake yi wa ciyawar jeji sutura, wadda yau tana nan, gobe kuwa a jefa a cikin wuta, ba zai ma fi yi muku sutura ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?
And if God clothith thus the hei of the feeld, that to day is, and to morewe is cast in to an ouen, hou myche more you of litel feith?
31 Don haka, kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci?’ Ko, ‘Me za mu sha?’ Ko kuma, ‘Me za mu sa?’
Therfor nyle ye be bisi, seiynge, What schulen we ete? or, What schulen we drinke? or, With what thing schulen we be keuered?
32 Gama marasa sanin Allah suna fama neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
For hethene men seken alle these thingis; and youre fadir woot, that ye han nede to alle these thingis.
33 Da farko dai, ku nemi mulkin Allah da kuma adalcinsa, za a kuwa ba ku dukan waɗannan abubuwa.
Therfor seke ye first the kyngdom of God, and his riytfulnesse, and alle these thingis shulen be cast to you.
34 Saboda haka kada ku damu game da gobe, gama gobe zai damu da kansa. Damuwar yau ma ta isa wahala.
Therfor nyle ye be bisy in to the morew, for the morew shal be bisi to `hym silf; for it suffisith to the dai his owen malice.

< Mattiyu 6 >