< Mattiyu 6 >

1 “Ku yi hankali kada ku nuna ‘ayyukanku na adalci’ a gaban mutane, don su gani. In kuka yi haka, ba za ku sami lada daga wurin Ubanku da yake cikin sama ba.
[But] take heed, that ye do not, your righteousness, before men, to be gazed at by them, —otherwise at least, reward, have ye none, with your Father who is in the heavens.
2 “Saboda haka sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yi shelarsa, yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan tituna, don mutane su yabe su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
When, therefore, thou mayest be doing an alms, do not sound a trumpet before thee, just as, the hypocrites, do in the synagogues and in the streets—that they may be glorified by men, —Verily, I say unto you, they are getting back their reward.
3 Amma sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yarda hannun hagunka yă ma san abin da hannun damarka yake yi,
But, thou, when doing an alms, let not, thy left hand, know what thy right hand is doing;
4 don bayarwarka ta zama a ɓoye. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
that thine alms may be in secret, —and, thy Father, who seeth in secret, will give it back to thee.
5 “Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku zama kamar munafukai, gama sun cika son yin addu’a a tsaye a cikin majami’u da kuma a bakin titi, don mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
And, when ye may be praying, ye shall not be as the hypocrites, because they love, in the synagogues, and at the corners of the broad ways, to take their stand and pray, that they may shine before men; Verily, I say unto you, they are getting back their reward.
6 Amma sa’ad da kake addu’a, sai ka shiga ɗakinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanka wanda ba a gani. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
But, thou, when thou wouldest pray, enter into thy closet, and, fastening thy door, pray unto thy Father who is in secret, —and, thy Father who seeth in secret, will reward thee.
7 Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku yi ta maimaita magana, kamar marasa sanin Allah, domin suna tsammani za a ji su saboda yawan maganarsu.
And, being at prayer, use not vain repetitions, just like the nations, —for they think, that, in their much speaking, they shall be hoard;
8 Kada ku zama kamar su, gama Ubanku ya san abin da kuke bukata kafin ma ku roƙe shi.
do not, therefore, make yourselves like them, for [God] your Father knoweth of what things ye have, need, before ye ask him.
9 “To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a. “‘Ubanmu wanda yake cikin sama, a tsarkake sunanka,
Thus, therefore pray, ye: Our Father, who art in the heavens, —Hallowed be thy name,
10 mulkinka yă zo a aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a sama.
Come may thy kingdom, —Accomplished be thy will, as in heaven, also on earth:
11 Ka ba mu yau abincin yininmu.
Our needful bread, give us, this day;
12 Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.
And forgive us our debts, as, we also, have forgiven our debtors;
13 Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
And bring us not into temptation, but rescue us from the evil one.
14 Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku.
For, if ye forgive men their faults, Your Father who is in the heavens, will forgive, even you;
15 Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.
But, if ye forgive not men [their faults], neither will your Father forgive, your faults.
16 “Sa’ad da kuma kuna azumi, kada ku ɓata fuska, yadda munafukai suke yi. Sukan ɓata fuskokinsu domin su nuna wa mutane cewa suna azumi. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
And, when ye may he fasting, become not ye, as the hypocrites, of sullen countenance, —for they darken their looks, that they may appear, unto men, to be fasting: Verily, I say unto you, they are getting back their reward.
17 Amma sa’ad da kana azumi, ka shafa wa kanka mai, ka wanke fuskarka,
But, when, thou, art fasting, anoint thy head, and, thy face, wash, —
18 domin kada mutane su ga alama cewa kana azumi, sai dai Ubanka kaɗai wanda ba a gani; Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
that thou do not appear, unto men, to be fasting, but to thy Father who is in secret, —and, thy Father who seeth in secret, will reward thee.
19 “Kada ku yi wa kanku ajiyar dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda kuma ɓarayi sukan fasa, su yi sata.
Be not laying up for yourselves treasures upon the earth, where, moth and rust, do tarnish, and where, thieves, dig through and steal;
20 Amma ku yi wa kanku ajiyar dukiya a sama, inda ba tsatsa da asu da za su ɓata su, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa, su yi sata.
but be laying up or yourselves treasures in heaven, where, neither moth nor rust, doth tarnish, and where, thieves, dig not through nor steal:
21 Gama inda dukiyarka take, a nan ne fa zuciyarka za tă kasance.
for, where, thy treasure, is, there, will be, thy heart [also].
22 “Ido shi ne fitilar jiki. In idanunka suna da kyau, dukan jikinka zai cika da haske.
The lamp of the body, is the eye: if therefore thine eye be single, thy whole body, shall be, lighted up;
23 Amma in idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma zai cika da duhu. To, in hasken da yake a cikinka duhu ne, duhun ya wuce misali ke nan!
But, if thine eye be, evil, thy whole body, shall be, in the dark; —if therefore, the light which is in thee, is, darkness, the darkness, how great!
24 “Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu. Ko dai yă ƙi ɗaya, yă ƙaunaci ɗaya, ko kuwa yă yi aminci ga ɗaya, sa’an nan yă rena ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah, ku kuma bauta wa kuɗi gaba ɗaya.”
No one, unto two masters, can be in service; for either, the one, he will hate, and, the other, love, or, one, he will hold to, and, the other, despise: Ye cannot be in service, unto God, and, unto Riches.
25 “Saboda haka, ina gaya muku, kada ku damu game da rayuwarku, game da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha; ko kuma game da jikinku, game da abin da za ku sa. Ashe, rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
For this cause, I say unto you: Be not anxious for your life, what ye shall eat [or what ye shall drink], —or for your body, what ye shall put on: Is not, the life, more than, the food? And, the body, than, the raiment?
26 Ku dubi tsuntsayen sararin sama mana; ba sa shuki ko girbi ko ajiya a rumbuna, duk da haka, Ubanku na sama yana ciyar da su. Ashe, ba ku fi su daraja nesa ba?
Observe intently, the birds of the heaven, —that they neither sow, nor reap, nor gather into barns, and yet, your heavenly Father, feedeth, them: Are no, ye, much better than, they?
27 Wane ne a cikinku ta wurin damuwa zai iya ƙara wa rayuwarsa ko sa’a ɗaya?
But who from among you, being anxious, can add to his stature one cubit?
28 “Me ya sa kuke damuwa a kan riguna? Ku dubi yadda furannin jeji suke girma mana. Ba sa aiki ko saƙa.
And, about clothing, why are ye anxious? Consider well the lilies of the field, how they grow, —they toil not neither do they spin;
29 Duk da haka ina gaya muku ko Solomon cikin dukan darajarsa bai sa kayan adon da ya kai na ko ɗaya a cikinsu ba.
And yet, I say unto you, not even Solomon, in all his glory, was arrayed like, one of these!
30 In haka Allah yake yi wa ciyawar jeji sutura, wadda yau tana nan, gobe kuwa a jefa a cikin wuta, ba zai ma fi yi muku sutura ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?
Now, if the grass of the field—which to-day, is, and, to-morrow, into an oven, is cast—God thus adorneth, not much rather, you, little of faith?
31 Don haka, kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci?’ Ko, ‘Me za mu sha?’ Ko kuma, ‘Me za mu sa?’
Do not then be anxious saying, What shall we eat? or What shall we drink? or Wherewithal shall we be arrayed?
32 Gama marasa sanin Allah suna fama neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
For, all these things, the nations, seek after, —for your heavenly Father, knoweth, that ye are needing, all these things.
33 Da farko dai, ku nemi mulkin Allah da kuma adalcinsa, za a kuwa ba ku dukan waɗannan abubuwa.
But be seeking first, the kingdom and its righteousness, —and, all these things, shall be added unto you.
34 Saboda haka kada ku damu game da gobe, gama gobe zai damu da kansa. Damuwar yau ma ta isa wahala.
Do not, then, be anxious for the morrow; for the morrow, will be anxious, for itself: Sufficient for the day, is the evil thereof.

< Mattiyu 6 >