< Mattiyu 5 >

1 Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa,
And seeing the multitudes He went up to a mountain, and when He was set down, His disciples came to Him,
2 sai ya fara koya musu. Yana cewa,
and He opened his mouth and taught them, saying,
3 “Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
Blessed are the poor in spirit; for theirs is the kingdom of heaven.
4 Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
Blessed are they that mourn; for they shall be comforted.
5 Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
Blessed are the meek; for they shall inherit the earth.
6 Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
Blessed are they that hunger and thirst after righteousness; for they shall be satisfied.
7 Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
Blessed are the merciful; for they shall obtain mercy.
8 Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
Blessed are the pure in heart; for they shall see God.
9 Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su’ya’yan Allah.
Blessed are the peace-makers; for they shall be called the children of God.
10 Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
Blessed are they, who are persecuted for righteousness sake; for theirs is the kingdom of heaven.
11 “Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni.
Blessed are ye when men shall revile and persecute you, and utter all manner of reproach against you falsly, for my sake:
12 Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.
rejoice and be exceeding glad; for great will be your reward in heaven: for so they persecuted the prophets, that were before you.
13 “Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.
Ye are the salt of the earth, but if the salt be grown insipid, wherewith shall it be seasoned? it is no longer fit for any thing, but to be thrown out of doors, and trodden under foot.
14 “Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa.
Ye are the light of the world: a city, that is situated on a hill, cannot be hid.
15 Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida.
Nor do men light a candle, to put it under a bushel, but on a candlestick: and then it giveth light to all in the house.
16 Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.
So let your light shine before men, that they may see your good works, and glorify your father, who is in heaven.
17 “Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su.
Think not that I am come to abrogate the law, or the prophets: I am not come to abolish, but to compleat them:
18 Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome.
for verily I say unto you, Till heaven and earth pass away, not one jot nor one tittle shall pass from the law, till all be compleated.
19 Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama.
Whosoever therefore shall break one of the left of these commandments, and thereby teach men so to do, he shall be esteemed very little in the kingdom of heaven: but whoever shall do as well as teach them, he shall be accounted great in the kingdom of heaven.
20 Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.
For I tell you, that unless your righteousness exceed that of the scribes and pharisees, ye shall not enter into the kingdom of heaven.
21 “Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai; kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
Ye have heard, that it was said to the ancients, Thou shalt not kill; and whosoever committeth murder, shall be liable to the judgment:
22 Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
but I say unto you, that whosoever is angry with his brother without cause shall be liable to the judgment; and whosoever shall say to his brother, Raca, shall be obnoxious to the council; but whosoever shall say, "Thou fool," shall be in danger of hell-fire. (Geenna g1067)
23 “Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
Therefore, if thou bring thine offering to the altar, and there remembrest that thy brother hath any complaint against thee;
24 sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
leave thy gift there before the altar, and go and first be reconciled to thy brother, and then come and offer thy gift.
25 “Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku.
Be friends with thine adversary quickly, while thou art in the way with him; least the adversary deliver thee to the judge, and the judge deliver thee to the officer, and thou be cast into prison:
26 Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.
verily, I say unto thee, thou shalt not come out from thence, till thou hast paid the very last farthing.
27 “Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’
Ye have heard, that it was said to the ancients, Thou shalt not commit adultery:
28 Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa.
but I tell you, that whosoever looketh on a woman, so as to lust after her, hath already debauched her in his heart.
29 In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
And therefore if thy right eye cause thee to offend, pluck it out and cast it from thee; for it is better for thee that one part of thee perish, than that thy whole body should be cast into hell: (Geenna g1067)
30 In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
and if thy right hand cause thee to offend, cut it off and cast it from thee; for it is better for thee that one of thy limbs should perish, than that thy whole body should be cast into hell. (Geenna g1067)
31 “An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’
And it has been said, whosoever would put away his wife, let him give her a bill of divorce:
32 Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.
but I say unto you, that whosoever shall put away his wife, except on account of whoredom, tempteth her to commit adultery; and if any man marry her that is divorced, he committeth adultery.
33 “Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’
Again, ye have heard, that it was said to the ancients, Thou shalt not forswear thyself, but shalt perform unto the Lord thine oaths:
34 Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne;
but I say unto you, swear not at all; neither by heaven, for it is the throne of God;
35 ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne.
nor by the earth, for it is his footstool; nor by Jerusalem, for it is the city of the great King: neither shalt thou swear by thy head,
36 Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba.
for thou canst not make one hair of it white or black:
37 Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.
but let your conversation be yea, yea; no, no; for whatever is more than these, cometh from the evil one.
38 “Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’
Ye have heard, that it has been said, An eye for an eye, and a tooth for a tooth:
39 Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma.
but I say unto you, Set not yourselves against him that injures you, but if any one smite thee on thy right cheek, rather turn to him the other also:
40 In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma.
and if any one would go to law with thee, to take away thy coat, let him have thy cloak also, rather than strive with him:
41 In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu.
and if any one shall force thee one mile, go with him two.
42 Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.
Give to him that asketh thee, and him, that would borrow of thee, turn not away.
43 “Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka, ka kuma ƙi abokin gābanka.’
Ye have heard, that it has been said, Thou shalt love thy neighbour, and hate thine enemy:
44 Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
but I say unto you, Love your enemies, bless them that curse you, do good to them that hate you, and pray for them that abuse you and persecute you;
45 don ku zama’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
that ye may be the children of your heavenly Father; for He causeth his sun to rise on the evil and the good, and sendeth rain upon the just and the unjust.
46 In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
For if ye love only them that love you, what reward do ye expect? do not even the publicans the same?
47 In kuwa kuna gai da’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
and if ye embrace your brethren only, what do ye more than others? do not the publicans so likewise?
48 Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.
Be ye therefore perfect in love and goodness, as your Father who is in heaven is perfect.

< Mattiyu 5 >