< Mattiyu 5 >

1 Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa,
When Jesus saw the crowds, he went up on the mountain. When he had sat down, his disciples came to him.
2 sai ya fara koya musu. Yana cewa,
He opened his mouth and taught them, saying,
3 “Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
“Blessed are the poor in spirit, for theirs is the kingdom of heaven.
4 Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
Blessed are those who mourn, for they will be comforted.
5 Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
Blessed are the meek, for they will inherit the earth.
6 Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
Blessed are those who hunger and thirst for righteousness, for they will be filled.
7 Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
Blessed are the merciful, for they will obtain mercy.
8 Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
Blessed are the pure in heart, for they will see God.
9 Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su’ya’yan Allah.
Blessed are the peacemakers, for they will be called sons of God.
10 Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
Blessed are those who have been persecuted for righteousness' sake, for theirs is the kingdom of heaven.
11 “Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni.
Blessed are you when people insult you and persecute you, and say all kinds of evil things against you falsely for my sake.
12 Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.
Rejoice and be very glad, for great is your reward in heaven. For in this way people persecuted the prophets who lived before you.
13 “Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.
You are the salt of the earth. But if the salt has lost its taste, how can it be made salty again? It is never again good for anything except to be thrown out and trampled under people's feet.
14 “Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa.
You are the light of the world. A city set on a hill cannot be hidden.
15 Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida.
Neither do people light a lamp and put it under a basket, but rather on the lampstand, and it shines for everyone in the house.
16 Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.
Let your light shine before people in such a way that they see your good deeds and praise your Father who is in heaven.
17 “Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su.
Do not think that I have come to destroy the law or the prophets. I have come not to destroy them, but to fulfill them.
18 Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome.
For truly I say to you that until heaven and earth pass away, not one jot or one tittle shall in any way pass away from the law, until all things have been accomplished.
19 Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama.
Therefore whoever breaks the least one of these commandments and teaches others to do so will be called least in the kingdom of heaven. But whoever keeps them and teaches them will be called great in the kingdom of heaven.
20 Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.
For I say to you that unless your righteousness exceeds the righteousness of the scribes and Pharisees, you will in no way enter the kingdom of heaven.
21 “Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai; kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
You have heard that it was said to them in ancient times, 'Do not kill,' and, 'Whoever kills will be in danger of the judgment.'
22 Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
But I say to you that everyone who is angry with his brother will be in danger of the judgment; and whoever says to his brother, 'You worthless person!' will be in danger of the council; and whoever says, 'You fool!' will be in danger of the fire of hell. (Geenna g1067)
23 “Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
Therefore if you are offering your gift at the altar and there remember that your brother has anything against you,
24 sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
leave your gift there in front of the altar, and go on your way. First be reconciled with your brother, and then come and offer your gift.
25 “Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku.
Agree with your accuser quickly while you are with him on the way to court, or your accuser may hand you over to the judge, and the judge may hand you over to the officer, and you may be thrown into prison.
26 Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.
Truly I say to you, you will never come out from there until you have paid the last bit of money you owe.
27 “Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’
You have heard that it was said, 'Do not commit adultery.'
28 Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa.
But I say to you that everyone who looks on a woman to lust after her has already committed adultery with her in his heart.
29 In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
If your right eye causes you to stumble, pluck it out and throw it away from you. For it is better for you that one of your body parts should perish than that your whole body should be thrown into hell. (Geenna g1067)
30 In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna g1067)
If your right hand causes you to stumble, cut it off and throw it away from you. For it is better for you that one of your body parts should perish than that your whole body should go into hell. (Geenna g1067)
31 “An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’
It was also said, 'Whoever sends his wife away, let him give her a certificate of divorce.'
32 Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.
But I say to you that everyone who divorces his wife, except for the cause of sexual immorality, makes her an adulteress. Whoever marries her after she has been divorced commits adultery.
33 “Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’
Again, you have heard that it was said to those in ancient times, 'Do not swear a false oath, but carry out your oaths to the Lord.'
34 Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne;
But I say to you, swear not at all, neither by heaven, for it is the throne of God;
35 ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne.
nor by the earth, for it is the footstool for his feet; nor by Jerusalem, for it is the city of the great King.
36 Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba.
Neither swear by your head, for you cannot make one hair white or black.
37 Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.
But let your speech be 'Yes, yes,' or 'No, no.' Anything that is more than this is from the evil one.
38 “Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’
You have heard that it was said, 'An eye for an eye, and a tooth for a tooth.'
39 Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma.
But I say to you, do not resist one who is evil. Instead, whoever strikes you on your right cheek, turn to him the other also.
40 In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma.
If anyone wishes to go to court with you and takes away your coat, let that person also have your cloak.
41 In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu.
Whoever compels you to go one mile, go with him two.
42 Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.
Give to anyone who asks you, and do not turn away from anyone who wishes to borrow from you.
43 “Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka, ka kuma ƙi abokin gābanka.’
You have heard that it was said, 'You must love your neighbor and hate your enemy.'
44 Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
But I say to you, love your enemies and pray for those who persecute you,
45 don ku zama’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
so that you may be sons of your Father who is in heaven. For he makes his sun to rise on the evil and the good, and sends rain on the just and the unjust.
46 In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
For if you love those who love you, what reward do you get? Do not even the tax collectors do the same thing?
47 In kuwa kuna gai da’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
If you greet only your brothers, what do you do more than others? Do not even the Gentiles do the same thing?
48 Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.
Therefore you must be perfect, as your heavenly Father is perfect.

< Mattiyu 5 >