< Mattiyu 4 >

1 Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi.
Alors Jésus fut emmené dans le désert par l’Esprit pour être tenté par le diable.
2 Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa.
Et ayant jeûné 40 jours et 40 nuits, après cela il eut faim.
3 Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”
Et le tentateur, s’approchant de lui, dit: Si tu es Fils de Dieu, dis que ces pierres deviennent des pains.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’”
Mais lui, répondant, dit: Il est écrit: « L’homme ne vivra pas de pain seulement, mais de toute parole qui sort de la bouche de Dieu ».
5 Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali.
Alors le diable le transporte dans la ville sainte, et le place sur le faîte du temple,
6 Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
et lui dit: Si tu es Fils de Dieu, jette-toi en bas, car il est écrit: « Il donnera des ordres à ses anges à ton sujet, et ils te porteront sur [leurs] mains, de peur que tu ne heurtes ton pied contre une pierre ».
7 Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
Jésus lui dit: Il est encore écrit: « Tu ne tenteras pas le Seigneur ton Dieu ».
8 Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
Le diable le transporte encore sur une fort haute montagne, et lui montre tous les royaumes du monde et leur gloire,
9 Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”
et lui dit: Je te donnerai toutes ces choses, si, te prosternant, tu me rends hommage.
10 Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’”
Alors Jésus lui dit: Va-t’en, Satan, car il est écrit: « Tu rendras hommage au Seigneur ton Dieu, et tu le serviras lui seul ».
11 Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.
Alors le diable le laisse: et voici, des anges s’approchèrent et le servirent.
12 Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili.
Or, ayant entendu dire que Jean avait été livré, il se retira en Galilée;
13 Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali
et ayant quitté Nazareth, il alla demeurer à Capernaüm, qui est au bord de la mer, sur les confins de Zabulon et de Nephthali,
14 don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,
afin que fût accompli ce qui avait été dit par Ésaïe le prophète, disant:
15 “Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun, wannan yankin Galili ta Al’ummai,
« Terre de Zabulon, et terre de Nephthali, chemin de la mer au-delà du Jourdain, Galilée des nations:
16 mutanen da suke zama cikin duhu sun ga babban haske; haske kuma ya haskaka a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”
le peuple assis dans les ténèbres a vu une grande lumière; et sur ceux qui sont assis dans la région et dans l’ombre de la mort, la lumière s’est levée ».
17 Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
Dès lors Jésus commença à prêcher et à dire: Repentez-vous, car le royaume des cieux s’est approché.
18 Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne.
Et comme il marchait le long de la mer de Galilée, il vit deux frères, Simon appelé Pierre, et André son frère, qui jetaient un filet dans la mer, car ils étaient pêcheurs;
19 Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.”
et il leur dit: Venez après moi, et je vous ferai pêcheurs d’hommes.
20 Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.
Et eux aussitôt, ayant laissé leurs filets, le suivirent.
21 Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su,
Et, passant de là plus avant, il vit deux autres frères, Jacques le [fils] de Zébédée, et Jean son frère, dans le bateau avec Zébédée leur père, raccommodant leurs filets, et il les appela;
22 nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.
et eux aussitôt, ayant quitté le bateau et leur père, le suivirent.
23 Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane.
Et Jésus parcourait toute la Galilée, enseignant dans leurs synagogues, et prêchant l’évangile du royaume, et guérissant toute sorte de maladies et toute sorte de langueurs parmi le peuple.
24 Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.
Et sa renommée se répandit dans toute la Syrie; et on lui amena tous ceux qui se portaient mal, qui étaient affligés de diverses maladies et de divers tourments, et des démoniaques, et des lunatiques, et des paralytiques, et il les guérit.
25 Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis, Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.
Et de grandes foules le suivirent de la Galilée, et de Décapolis, et de Jérusalem, et de Judée, et de par-delà le Jourdain.

< Mattiyu 4 >