< Mattiyu 3 >

1 A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
tadAnoM yohnnAmA majjayitA yihUdIyadeshasya prAntaram upasthAya prachArayan kathayAmAsa,
2 yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
manAMsi parAvarttayata, svargIyarAjatvaM samIpamAgatam|
3 Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
parameshasya panthAnaM pariShkuruta sarvvataH| tasya rAjapathAMshchaiva samIkuruta sarvvathA| ityetat prAntare vAkyaM vadataH kasyachid ravaH||
4 Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
etadvachanaM yishayiyabhaviShyadvAdinA yohanamuddishya bhAShitam| yohano vasanaM mahA NgaromajaM tasya kaTau charmmakaTibandhanaM; sa cha shUkakITAn madhu cha bhuktavAn|
5 Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
tadAnIM yirUshAlamnagaranivAsinaH sarvve yihUdideshIyA yarddantaTinyA ubhayataTasthAshcha mAnavA bahirAgatya tasya samIpe
6 Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
svIyaM svIyaM duritam a NgIkR^itya tasyAM yarddani tena majjitA babhUvuH|
7 Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
aparaM bahUn phirUshinaH sidUkinashcha manujAn maMktuM svasamIpam AgachChto vilokya sa tAn abhidadhau, re re bhujagavaMshA AgAmInaH kopAt palAyituM yuShmAn kashchetitavAn?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
manaHparAvarttanasya samuchitaM phalaM phalata|
9 Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
kintvasmAkaM tAta ibrAhIm astIti sveShu manaHsu chIntayanto mA vyAharata| yato yuShmAn ahaM vadAmi, Ishvara etebhyaH pAShANebhya ibrAhImaH santAnAn utpAdayituM shaknoti|
10 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
aparaM pAdapAnAM mUle kuThAra idAnImapi lagan Aste, tasmAd yasmin pAdape uttamaM phalaM na bhavati, sa kR^itto madhye. agniM nikShepsyate|
11 “Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
aparam ahaM manaHparAvarttanasUchakena majjanena yuShmAn majjayAmIti satyaM, kintu mama pashchAd ya AgachChati, sa mattopi mahAn, ahaM tadIyopAnahau voDhumapi nahi yogyosmi, sa yuShmAn vahnirUpe pavitra Atmani saMmajjayiShyati|
12 Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
tasya kAre sUrpa Aste, sa svIyashasyAni samyak prasphoTya nijAn sakalagodhUmAn saMgR^ihya bhANDAgAre sthApayiShyati, kiMntu sarvvANi vuShANyanirvvANavahninA dAhayiShyati|
13 Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
anantaraM yIshu ryohanA majjito bhavituM gAlIlpradeshAd yarddani tasya samIpam AjagAma|
14 Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
kintu yohan taM niShidhya babhAShe, tvaM kiM mama samIpam AgachChasi? varaM tvayA majjanaM mama prayojanam Aste|
15 Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
tadAnIM yIshuH pratyavochat; IdAnIm anumanyasva, yata itthaM sarvvadharmmasAdhanam asmAkaM karttavyaM, tataH so. anvamanyata|
16 Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
anantaraM yIshurammasi majjituH san tatkShaNAt toyamadhyAd utthAya jagAma, tadA jImUtadvAre mukte jAte, sa IshvarasyAtmAnaM kapotavad avaruhya svoparyyAgachChantaM vIkShA nchakre|
17 Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”
aparam eSha mama priyaH putra etasminneva mama mahAsantoSha etAdR^ishI vyomajA vAg babhUva|

< Mattiyu 3 >