< Mattiyu 3 >
1 A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
In those days appeared John the Immerser, who proclaimed in the wilderness of Judea, saying,
2 yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
Reform, for the Reign of Heaven approaches.
3 Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
For this is he, of whom the Prophet Isaiah speaks in these words, "The voice of one proclaiming in the wilderness, Prepare a way for the Lord, make for him a straight passage."
4 Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
Now John wore raiment of camel's hair with a letter girdle about his waist; and his food was locusts and wild honey.
5 Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
Then Jerusalem, and all Judea, and all the country along the Jordan, resorted to him,
6 Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
and were immersed by him in the Jordan, confessing their sins.
7 Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
But he seeing many Pharisees and Sadducees coming to him to receive immersion, said to them, Offspring of vipers, who has prompted you to flee from the impending vengeance?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
Produce, then, the proper fruit of reformation;
9 Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
and presume not to say within yourselves, We have Abraham for our father, for I assure you, that of these stones God can raise children to Abraham.
10 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
And even now the ax lies at the root of the trees; every tree, therefore, which produces not good fruit, is cut down, and turned into fuel.
11 “Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
I, indeed, immerse you in water, into reformation; but he who comes after me, is mightier than I, whose shoes I am not worthy to carry. He will immerse you in the Holy Spirit, and in fire.
12 Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
His winnowing shovel is in his hand, and he will thoroughly cleanse his grain; he will gather his wheat into the granary, and consume the chaff in unquenchable fire.
13 Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
Then came Jesus from Galilee to the Jordan, to be immersed by John.
14 Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
But John excused himself, saying, It is I who need to be immersed by you; and you come to me!
15 Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
Jesus answering, said to him, Permit this at present; for thus ought we to ratify every institution. Then John acquiesced.
16 Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
Jesus being immersed, no sooner arose out of the water, than heaven was opened to him; and the Spirit of God appeared, descending like a dove, and lighting upon him;
17 Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”
while a voice from heaven proclaimed, This is my Son, the beloved, in whom I delight.