< Mattiyu 3 >

1 A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
Now in those days John the Baptizer began preaching in the wilderness of Judea
2 yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
and saying, “Repent, for the kingdom of the heavens has come near!”
3 Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
For this is he who was referred to by the prophet Isaiah, saying: “A voice crying-out, ‘Prepare in the wilderness the way of the Lord, make His paths straight.’”
4 Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
Now John actually used clothes made from camel's hair and a leather belt around his waist; while his food was locusts and wild honey.
5 Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
Then Jerusalem, all Judea and all the region of the Jordan went out to him,
6 Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
and were being baptized by him in the Jordan, confessing their sins.
7 Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
But seeing many of the Pharisees and Sadducees coming to his baptism, he said to them: “Brood of vipers! Who tipped you off to flee from the coming wrath?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
Therefore produce fruit worthy of repentance,
9 Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
and don't even think to say within yourselves, ‘We have Abraham as father,’ for I say to you that God is able to raise up children to Abraham from these stones.
10 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
Indeed, already the ax is being laid to the root of the trees. So every tree not producing good fruit is cut down and thrown into the fire.
11 “Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
“I baptize you with water unto repentance, but the One coming after me is mightier than I, whose sandals I am not worthy to carry. He will baptize you with Holy Spirit.
12 Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
His winnowing shovel is in His hand, and He will thoroughly clean out His threshing floor and gather His wheat into the barn; but He will burn up the chaff with unquenchable fire.”
13 Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
Then Jesus came from Galilee to John at the Jordan to be baptized by him.
14 Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
But John tried to dissuade Him saying, “I have need to be baptized by You, and You are coming to me?”
15 Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
But in answer Jesus said to him, “Permit it now, because thus it is appropriate to us to fulfill all righteousness.” Then he permitted Him.
16 Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
And having been baptized Jesus came up directly from the water, when wow, the heavens were opened to Him, and he saw the Spirit of God coming down like a dove and alighting upon Him.
17 Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”
And wow, a Voice from the heavens saying, “This is my Son, the beloved, in whom I am always well pleased!”

< Mattiyu 3 >