< Mattiyu 3 >
1 A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
In those days came John the Immerser, preaching in the wilderness of Judea,
2 yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
and saying: Repent, for the kingdom of heaven is at hand.
3 Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
For this is he that was spoken of by Isaiah the prophet, saying: The voice of one crying in the wilderness, Prepare the way of the Lord, make his paths straight.
4 Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
But the same John had his clothing of camel’s hair, and a girdle of leather around his loins, and his food was locusts and wild honey.
5 Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
Then went out to him Jerusalem, and all Judea, and all the region round about the Jordan,
6 Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
and were immersed by him in the Jordan, confessing their sins.
7 Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
But when he saw many of the Pharisees and Sadducees coming to his immersion, he said to them: Generation of vipers, who has warned you to flee from the coining wrath?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
Bring forth, therefore, fruit worthy of repentance:
9 Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
and think not to say within yourselves, We have Abraham for our father; for I say to you that God is able from these stones to raise up children to Abraham.
10 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
Even now the ax is lying at the root of the trees: therefore, every tree that does not bring forth good fruit is cut down and thrown into the fire.
11 “Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
I immerse you in water, in order to repentance; but he that comes after me is mightier than I, whose sandals I am not worthy to carry. He will immerse you in the Holy Spirit and in fire:
12 Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
whose winnowing-shovel is in his hand, and he will thoroughly cleanse his thrashing-floor, and gather his grain into his granary; but the chaff he will burn with unquenchable fire.
13 Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
Then came Jesus from Galilee to the Jordan to John, to be immersed by him.
14 Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
But John forbade him, saying: I have need to be immersed by thee, and comest thou to me?
15 Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
But Jesus answering said to him: Permit it now; for thus it becomes us to perform fully every righteous act. Then he permitted him.
16 Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
And after Jesus was immersed, he came up immediately from the water; and lo, the heavens were opened to him, and he saw the Spirit of God descending like a dove, and coming upon him.
17 Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”
And lo, a voice from heaven, saying: This is my beloved Son, in whom I delight.