< Mattiyu 28 >
1 Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.
Sambatay adhidappe guye samintappe koyro galas buro saloy zo7ishin Magidale Marama hara Maramakka dufoza beyana bida.
2 Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai.
Qopponta dishin gitta bitta qathi hanidees, Godda gitanchaykka salloppe wodhi dufakko bidi shucha gendesidi iza bolla utidees.
3 Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara.
Kitanchas medhay wolqantha po7o mala, mayoykka shacha mala bo7otu.
4 Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.
Dufo nagizayti kitanchazas babidi kokoridinne hayqeth milatida.
5 Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne.
Kitanachay macashata baboppite inte kaqetida Yesusa koyzasa ta erays izi ha7i han bawa,
6 Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta.
izi kasse yotida mala hayqoppe dendidees ha yidi izi zin7idaso beyte gidees.
7 Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”
Ha7ikka eleli bidi iza kalizaytas hayqoppe dendidees intefe kasetidi Galila bees, inte iza hen demana gidi yotite hi7a ta intes yotidas.
8 Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa.
Macashatikka babonine ufaysan kumidi iza kalizaytas yotanas elelidi wothan dufoy dizaso yegi agidi bida.
9 Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada.
Herakka Yesusay ista demidi hayto saro gidees. Istika Yesusakko shiqidine iza to oykidi izas goynida.
10 Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”
Yesusay ista babofite bidine isti Galila banal mala ta ishatas yotite. Istti tana hen beyana gidees.
11 Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru.
Macashati buro ogge bolla dishin nagizaytappe gutha bagati katama bidi hanidaysa wursi qesista halaqatas yotida.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa.
Qessista halaqatikka dere cimatara shiqetidi zoretida,
13 Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’
wotadaratas gidiza miish immidi nuni zin7on dishin iza kalizayti qammara yidi kaysi efida gite gida.
14 In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.”
Haysi worey dere harizaysa matan siyetikokka nuni izas lo7othi yotana, aykko itaykka inte bolla gakkonta mala nu ootha gida.
15 Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
Wotadaratikka misha ekkidi isti gida mala oothida, haysi yozi hach gakanas Ayhudata achan daro son yotetishe dees.
16 Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu.
Hessappekka Yesusa kaliza tamane issineti Yesusay issta besida Galilan diza zumma bolla kezida.
17 Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
Yesusa be7idamala izas goynida, ista grasappe guxiza batati sidhida.
18 Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa.
Yesusaykka bena kalizaytakko shiqidi salonine bitta bollan godatethi tass immetidees.
19 Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikinsunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki,
Hessa gish bidi dere wursos Aawa Na7azane Xillo Ayana suthan xamaqishe tana kalizayta oothite,
20 kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn )
ta intena azazidaysa wursi nagana mala tamarsitte takka alame wurseth gakanas ta intenara daysi gidees. (aiōn )