< Mattiyu 28 >
1 Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.
And, late in the week, when it was on the point of dawning into the first of the week, came Mary the Magdalene, and the other Mary, to view the sepulchre.
2 Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai.
And lo! a great commotion occurred, —for, a messenger of the Lord, descending out of heaven, and coming near, had rolled away the stone, and was sitting upon it.
3 Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara.
Now his appearance, was, as lightning, and, his clothing, white as snow;
4 Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.
and, for fear of him, they who were keeping watch were thrown into a commotion, and became as dead men.
5 Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne.
But the messenger, answering, said unto the women—Be not, ye, afraid! For I know that, Jesus the crucified, ye are seeking:
6 Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta.
He is not here, for he hath arisen, as he said. Come! see the place where he lay;
7 Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”
And, quickly going, tell his disciples—He hath arisen from the dead, and lo! he is going before you into Galilee; —There, shall ye yourselves see him: Lo! I have told you.
8 Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa.
And, departing quickly from the tomb with fear and great joy, they ran to bring tidings unto his disciples.
9 Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada.
And lo! Jesus, met them, saying—Joy to you! And, they, going forward, held his feet, and worshipped him.
10 Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”
Then, Jesus saith unto them—Be not afraid! Go your way, bear tidings unto my brethren, that they may depart into Galilee; and, there, shall they themselves see me.
11 Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru.
Now as they were, going, lo! certain of the guard, went into the city and reported unto the High-priests all the things that had come to pass;
12 Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa.
and, being gathered together with the Elders and taking counsel, sufficient pieces of silver, gave they unto the soldiers, —
13 Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’
saying—Say ye, His disciples, coming, by night, stole him, while we were sleeping;
14 In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.”
And, if this be reported unto the governor, we, will persuade him, and will make, you, free from care.
15 Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
And, they, taking the pieces of silver, did as they were instructed. And this account was spread abroad among the Jews…until this [very] day.
16 Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu.
And, the eleven disciples, went into Galilee, unto the mountain which, Jesus, had appointed them;
17 Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
and, seeing him, they worshipped, but, some, doubted.
18 Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa.
And Jesus, coming near, spake unto them, saying—All authority, in heaven and on earth, hath been given unto me;
19 Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikinsunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki,
Go ye, therefore, and disciple all the nations, Immersing them into the name of the Father, and of the Son, and of the Holy Spirit, —
20 kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn )
Teaching them to observe all things whatsoever I myself have commanded you, And lo! I, am, with you, all the days, until the conclusion of the age. (aiōn )