< Mattiyu 28 >

1 Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.
And after the sabbath, as it began to dawn toward the first day of the week, Mary Magdalene and the other Mary came to see the sepulcher.
2 Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai.
And behold, there had been a great earthquake; for an angel of the Lord having descended from heaven, came and rolled away the stone from the door, and sat upon it.
3 Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara.
His appearance was like lightning, and his raiment was white as snow.
4 Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.
From fear of him the keepers did shake and become like dead men.
5 Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne.
But the angel answered and said to the women: Fear not; for I know that you seek Jesus, who was crucified.
6 Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta.
He is not here; for he has risen, as he said. Come, see the place where the Lord lay.
7 Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”
And go quickly, and tell his disciples, that he has risen from the dead: and behold, he goes before you into Galilee. There you shall see him. Lo, I have told you.
8 Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa.
And they went out quickly from the sepulcher, with fear and great joy, and ran to tell his disciples.
9 Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada.
And as they were going to tell his disciples, behold, Jesus met them, saying: Hail! And they came and laid hold of his feet, and worshiped him.
10 Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”
Then Jesus said to them: Fear not; go, tell my brethren to go into Galilee, and there they shall see me.
11 Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru.
While they were going, behold, some of the guard came into the city, and told the chief priests all things that were done.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa.
And when they came together with the elders, they held a consultation, and gave much money to the soldiers,
13 Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’
saying: Say that his disciples came by night and stole him away, while we were asleep.
14 In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.”
And if this shall be heard in the presence of the governor, we will persuade him, and make you secure.
15 Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
And they took the money, and did as they were taught. And their report of this matter is everywhere published among the Jews to this day.
16 Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu.
And the eleven disciples went away into Galilee, into the mountain, where Jesus had appointed to meet them.
17 Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
And when they saw him, they worshiped him; but some doubted.
18 Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa.
And Jesus came and spoke to them, saying: All authority in heaven and on earth is given to me.
19 Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikinsunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki,
Go, therefore, make disciples of all nations, immersing them (the disciples) into the name of the Father, and of the Son, and of the Holy Spirit;
20 kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn g165)
teaching them to observe all things whatever I have commanded you: and lo; I am with you all the days, even to the end of the age. (aiōn g165)

< Mattiyu 28 >