< Mattiyu 28 >

1 Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.
Po suboti, u osvit prvoga dana u tjednu, dođe Marija Magdalena i druga Marija pogledati grob.
2 Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai.
I gle, nastade žestok potres jer anđeo Gospodnji siđe s neba, pristupi, otkotrlja kamen i sjede na nj.
3 Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara.
Lice mu bijaše kao munja, a odjeća bijela kao snijeg.
4 Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.
Od straha pred njim zadrhtaše stražari i obamriješe.
5 Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne.
A anđeo progovori ženama: “Vi se ne bojte! Ta znam: Isusa Raspetoga tražite!
6 Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta.
Nije ovdje! Uskrsnu kako reče. Hajde, vidite mjesto gdje je ležao
7 Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”
pa pođite žurno i javite njegovim učenicima da uskrsnu od mrtvih. I evo, ide pred vama u Galileju. Ondje ćete ga vidjeti. Evo, rekoh vam.”
8 Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa.
One otiđoše žurno s groba te sa strahom i velikom radošću otrčaše javiti njegovim učenicima.
9 Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada.
Kad eto im Isusa u susret! Reče im: “Zdravo!” One polete k njemu, obujme mu noge i ničice mu se poklone.
10 Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”
Tada im Isus reče: “Ne bojte se! Idite, javite mojoj braći da pođu u Galileju! Ondje će me vidjeti!”
11 Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru.
Dok su one odlazile, gle, neki od straže dođoše u grad i javiše glavarima svećeničkim sve što se dogodilo.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa.
Oni se sabraše sa starješinama na vijećanje, uzeše mnogo novaca i dadoše vojnicima
13 Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’
govoreći: “Recite: 'Noću dok smo mi spavali, dođoše njegovi učenici i ukradoše ga.'
14 In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.”
Ako to dočuje upravitelj, mi ćemo ga uvjeriti i sve učiniti da vi budete bez brige.”
15 Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
Oni uzeše novac i učiniše kako bijahu poučeni. I razglasilo se to među Židovima - sve do danas.
16 Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu.
Jedanaestorica pođoše u Galileju na goru kamo im je naredio Isus.
17 Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
Kad ga ugledaše, padoše ničice preda nj. A neki posumnjaše.
18 Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa.
Isus im pristupi i prozbori: “Dana mi je sva vlast na nebu i na zemlji!
19 Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikinsunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki,
Pođite dakle i učinite mojim učenicima sve narode krsteći ih u ime Oca i Sina i Duha Svetoga
20 kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn g165)
i učeći ih čuvati sve što sam vam zapovjedio!” “I evo, ja sam s vama u sve dane - do svršetka svijeta.” (aiōn g165)

< Mattiyu 28 >