< Mattiyu 27 >
1 Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
And when it was morning, all the chief priests and the elders of the people consulted together against Jesus, to put him to death.
2 Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
And having bound him, they led him away, and delivered him up to Pilate the governor.
3 Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
Then Judas, who betrayed him, when he saw that he was condemned, repented, and brought back the thirty pieces of silver to the chief priests and elders,
4 Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
saying, I sinned in betraying innocent blood. And they said, What is that to us? See thou to it.
5 Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
And he cast down the pieces of silver in the temple, and withdrew; and went away and hanged himself.
6 Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
And the chief priests took the pieces of silver, and said, It is not lawful to put them into the treasury, since they are the price of blood.
7 Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
And they consulted together, and bought with them the potter's field, for a burial-place for strangers.
8 Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
Wherefore that field hath been called, The Field of Blood, unto this day.
9 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
Then was fulfilled that which was spoken through Jeremiah the prophet, saying, “And they took the thirty pieces of silver, the price of him that was priced, whom they of the sons of Israel priced,
10 suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
and gave them for the potter's field; as the Lord commanded me.”
11 Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
And Jesus stood before the governor; and the governor questioned him, saying, Art thou the king of the Jews? And Jesus said, I am.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
And when he was accused by the chief priests and elders, he made no answer.
13 Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
Then saith Pilate to him, Dost thou not hear what things they are testifying against thee?
14 Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
And he made him no answer, not even to one word; so that the governor greatly wondered.
15 A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
Now at the feast the governor was wont to release to the multitude one prisoner, whom they would.
16 To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
And they had then a notorious prisoner, called Barabbas.
17 Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
When therefore they were assembled, Pilate said to them, Whom will ye that I release to you? Barabbas, or Jesus, who is called Christ?
18 Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
For he knew that for envy they had delivered him up.
19 Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
And while he was sitting on the judgment-seat, his wife sent to him, saying, Have nothing to do with that righteous man; for I have suffered much this day in a dream because of him.
20 Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
But the chief priests and the elders persuaded the multitudes to ask for Barabbas, and to destroy Jesus.
21 Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
And the governor answering said to them, Which of the two will ye that I release to you? And they said, Barabbas.
22 Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
Pilate saith to them, What then shall I do with Jesus, who is called Christ? They all say, Let him be crucified.
23 Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
And he said, Why, what evil hath he done? But they cried out the more, saying, Let him be crucified.
24 Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
And when Pilate saw that it availed nothing, but that rather a tumult was arising, he took water, and washed his hands before the multitude, saying, I am innocent of this blood; see ye to it.
25 Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
And all the people answering said, His blood be on us, and on our children.
26 Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
Then he released Barabbas to them, and having scourged Jesus, he delivered him up to be crucified.
27 Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
Then the soldiers of the governor took Jesus into the governor's palace, and gathered to him the whole band.
28 Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
And they stripped him, and put on him a scarlet robe.
29 Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
And having platted a crown of thorns, they put it on his head, and a reed in his right hand; and bowing the knee before him, they mocked him, saying, Hail, king of the Jews!
30 Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
And they spit upon him, and took the reed and struck him on the head.
31 Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
And after they had made sport of him, they took off the robe from him, and put on him his own garments, and led him away to crucify him.
32 Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
And as they were going out, they found a man of Cyrene, Simon by name, whom they compelled to carry his cross.
33 Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
And having come to a place called Golgotha, that is, Place of a Skull,
34 A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
they gave him wine to drink mingled with gall; and when he had tasted it, he refused to drink.
35 Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
And when they had crucified him, they divided his garments among them, casting lots.
36 Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
And sitting down, they watched him there.
37 Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
And they set up over his head the charge against him in writing: “This is Jesus the king of the Jews.”
38 An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
Then are crucified with him two robbers, one on the right hand, and one on the left.
39 Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
And they who passed by reviled him, wagging their heads,
40 suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
and saying, Thou that destroyest the temple, and buildest it up in three days, save thyself, if thou art the Son of God, and come down from the cross.
41 Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
So also the chief priests, mocking, with the scribes and elders, said,
42 “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
He saved others, cannot he save himself? He is the king of Israel, let him now come down from the cross, and we will believe in him.
43 Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
He trusteth in God; let him now deliver him, if he desireth him; for he said, I am the Son of God.
44 Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
The robbers also, who were crucified with him, reviled him in the same manner.
45 Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
And from the sixth hour there was darkness over all the land, until the ninth hour.
46 Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
And about the ninth hour Jesus cried with a loud voice, saying, Eli, Eli, lema sabachthani? that is to say, My God, my God, why hast thou forsaken me?
47 Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
Some of those standing there, when they heard this, said, This man is calling for Elijah.
48 Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
And one of them immediately ran and took a sponge, and filled it with vinegar, and put it on a reed, and gave it to him to drink.
49 Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
But the rest said, Hold! let us see whether Elijah will come to save him.
50 Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
And Jesus, crying out again with a loud voice, yielded up his spirit.
51 A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
And, lo! the veil of the temple was rent in two from the top to the bottom; and the earth, quaked, and the rocks were rent,
52 Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
and the tombs were opened; and many bodies of holy men that slept, arose,
53 Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
and coming out of the tombs after his resurrection went into the holy city and appeared to many.
54 Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
And the centurion and they who with him were watching Jesus, when they saw the earthquake, and what was taking place, were exceedingly afraid, saying, Truly this was the Son of God.
55 Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
And many women were there, looking on from a distance, who had followed Jesus from Galilee, rendering services to him;
56 A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
among whom was Mary the Magdalene, and Mary the mother of James and Joseph, and the mother of the sons of Zebedee.
57 Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
And at evening there came a rich man of Arimathaea, named Joseph, who was himself also a disciple of Jesus.
58 Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
This man went to Pilate, and asked for the body of Jesus. Then Pilate ordered it to be given him.
59 Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
And Joseph took the body, and wrapped it in a clean linen cloth,
60 Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
and laid it in his own new tomb, which he had hewn out in the rock, and having rolled a great stone to the door of the tomb, went away.
61 Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
And Mary the Magdalene was there, and the other Mary, sitting over against the sepulchre.
62 Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
And on the next day, that following the day of the preparation, the chief priests and the Pharisees came together to Pilate,
63 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
saying, Sir, we remember that that deceiver said, while he was yet alive, After three days I rise.
64 Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
Command therefore that the sepulchre be made secure until the third day, lest his disciples come and steal him away, and say to the people, He hath risen from the dead; and the last error will be worse than the first.
65 Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
Pilate said to them, Ye have a guard; go, make it as secure as ye know how.
66 Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.
And they went, and made the sepulchre secure, sealing the stone, and setting the guard.