< Mattiyu 27 >

1 Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
But having become morning, all the chief priests and the elders of the people held consultation against Jesus in order to condemn him to death.
2 Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
And having bound him, they led him away and delivered him to Pontius Pilate the governor.
3 Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
Then Judas, who betrayed him, after seeing that he was condemned, having repented, he brought back the thirty silver pieces to the chief priests and elders,
4 Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
saying, I sinned, having betrayed innocent blood. But they said, What is it to us? See thou to it.
5 Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
And having cast down the silver pieces in the temple, he departed, and after going away, he hanged himself.
6 Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
And after taking the silver pieces, the chief priests said, It is not permitted to put them into the treasury, since it is a price of blood.
7 Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
And having held consultation, they bought the potter's field with them for burial for foreigners.
8 Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
Therefore that field was called the field of blood, to this day.
9 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
Then that which was spoken through Jeremiah the prophet was fulfilled, which says, And they took the thirty silver pieces, the price of him who was valued, whom they valued from the sons of Israel,
10 suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
and they gave them for the potter's field, as the Lord appointed me.
11 Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
Now Jesus stood before the governor, and the governor questioned him, saying, Are thou the king of the Jews? And Jesus said to him, Thou say.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
And when he was accused by the chief priests and elders, he answered nothing.
13 Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
Then Pilate says to him, Do thou not hear how many things they testify against thee?
14 Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
And he did not answer him, not even one word, so as for the governor to marvel greatly.
15 A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
Now during a feast the governor had been accustomed to release to the crowd one prisoner whom they wanted.
16 To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
And they had then a notorious prisoner called Barabbas.
17 Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
When therefore they were gathered together, Pilate said to them, Whom do ye want I should release to you? Barabbas, or Jesus who is called Christ?
18 Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
For he knew that they delivered him up because of envy.
19 Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
And while he was sitting on the judgment seat, his wife sent to him, saying, There is nothing for thee and that righteous man. For I suffered many things this day in a dream because of him.
20 Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
But the chief priests and the elders persuaded the multitudes that they should ask for Barabbas, and destroy Jesus.
21 Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
Now the governor having answered, he said to them, Which of the two do ye want I would release to you? And they said, Barabbas.
22 Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
Pilate says to them, What then shall I do to Jesus who is called Christ? They all say to him, He should be crucified.
23 Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
And the governor said, For what evil has he done? But they cried out even more, saying, He should be crucified.
24 Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
And when Pilate saw that he was accomplishing nothing, but rather an uproar was developing, after taking water, he washed his hands in front of the multitude, saying, I am innocent of the blood of this righteous man. See ye to it.
25 Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
And having answered, all the people said, His blood be on us, and on our children.
26 Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
Then he released Barabbas to them, and having scourged Jesus he delivered him so that he would be crucified.
27 Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
Then the soldiers of the governor, having taken Jesus into the Praetorium, gathered the whole band to him.
28 Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
And having stripped him, they put a scarlet robe on him.
29 Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
And having woven a crown of thorns, they put it upon his head, and a reed in his right hand. And having knelt down before him, they ridiculed him, saying, Hail, king of the Jews!
30 Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
And having spat upon him, they took the reed and were striking him on his head.
31 Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
And after they ridiculed him, they took the robe off of him, and put his clothes on him, and led him away in order to crucify.
32 Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
And while coming out, they found a man of Cyrene, Simon by name. They drafted this man, so that he might take his cross.
33 Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
And having come to a place called Golgotha, that is called, the place of a skull,
34 A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
they gave him vinegar to drink mingled with gall. And having tasted it, he would not drink.
35 Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
And when they crucified him, they divided his garments, casting a lot.
36 Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
And as they sat, they keep watch over him there.
37 Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
And they set up over his head his accusation written, THIS IS JESUS THE KING OF THE JEWS.
38 An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
Then two robbers are crucified with him, one at the right hand and one at the left.
39 Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
And those who passed by reviled him, shaking their heads,
40 suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
and saying, Thou who destroy the temple, and build it in three days, save thyself. If thou are the Son of God, come down from the cross.
41 Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
And likewise also the chief priests, ridiculing with the scholars, and elders, and Pharisees, said,
42 “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
He saved others, he cannot save himself. If he is the king of Israel, let him now come down from the cross, and we will believe in him.
43 Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
He trusted in God, let him rescue him now, if he wants him, for he said, I am the Son of God.
44 Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
And also the robbers who were crucified with him reviled him the same way.
45 Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
Now from the sixth hour darkness developed over all the land until the ninth hour.
46 Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
And about the ninth hour Jesus cried out in a great voice, saying, Eli, Eli, lama sabachthani? That is, My God, my God, why have thou forsaken me?
47 Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
And some of those who stood there, when they heard it, said, This man calls Elijah.
48 Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
And straightaway one of them, after running, and having taken a sponge, and having filled it with vinegar, put it on a reed, and gave him to drink.
49 Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
But the others said, Leave thou be. We might see if Elijah comes he will save him.
50 Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
And Jesus, having cried out again in a great voice, yielded up his spirit.
51 A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
And behold, the curtain of the temple was torn in two from the top to the bottom, and the earth quaked, and the rocks split,
52 Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
and the sepulchers were opened, and many bodies of the sanctified who have been asleep arose.
53 Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
And having come forth out of the sepulchers after his resurrection they entered into the holy city and appeared to many.
54 Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
Now the centurion, and those with him watching over Jesus, when they saw the earthquake, and the things that happened, they feared greatly, saying, Truly this was the Son of God.
55 Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
And many women were there watching from afar, who followed Jesus from Galilee, serving him,
56 A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
among whom was Mary Magdalene, and Mary the mother of James and Joses, and the mother of the sons of Zebedee.
57 Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
And having become evening, there came a rich man from Arimathaea, named Joseph, who also himself was discipled by Jesus.
58 Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
This man having come to Pilate, requested the body of Jesus. Then Pilate commanded the body to be given.
59 Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
And Joseph having taken the body, wrapped it in a clean linen cloth,
60 Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
and laid it in his own new sepulcher, which he hewed out in the rock. And having rolled a great stone to the door of the sepulcher, he departed.
61 Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
And Mary Magdalene, and the other Mary were there, sitting opposite the tomb.
62 Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
Now on the morrow, which is after the Preparation, the chief priests and the Pharisees came together to Pilate,
63 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
saying, Sir, we remember that that deceiver said while he was still alive, After three days I am raised.
64 Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
Command therefore to secure the tomb until the third day, lest his disciples having come by night steal him away, and say to the people, He was raised from the dead. And the last error will be worse than the first.
65 Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
Pilate said to them, Ye have security. Go, make it as secure as ye know how.
66 Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.
And having gone, they made the tomb secure, with the security having sealed the stone.

< Mattiyu 27 >