< Mattiyu 27 >

1 Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
Ráno se opět sešli členové židovské velerady a domlouvali se, jak by přiměli Římany, aby potvrdili rozsudek smrti.
2 Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
Potom poslali spoutaného Ježíše k římskému místodržiteli Pilátovi.
3 Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
Když Jidáš viděl, že Ježíše odsoudili k smrti, hnulo se v něm svědomí, že ho zradil. Vzal třicet stříbrných, které dostal za zradu, a chtěl je vrátit představitelům velerady:
4 Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
„Zhřešil jsem, zradil jsem nevinného člověka!“Oni však lhostejně odpověděli: „Do toho nám nic není, to je tvoje věc!“
5 Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
Jidáš odhodil peníze v chrámu, vyběhl ven a oběsil se.
6 Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
Velekněží dali peníze sebrat a řekli si: „Co s nimi? Pro chrámovou pokladnu se nehodí. Lpí na nich krev!“
7 Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
Dohodli se tedy, že za ně koupí pozemek, kde si dříve hrnčíři kopali hlínu, a že tam budou pohřbívat cizince, kteří zemřou v Jeruzalémě.
8 Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
A tak se tomu místu až dodnes říká „Krvavé pole“.
9 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
Tím se splnilo staré proroctví: „Vzali třicet stříbrňáků – náhradu za život otroka, na kterou ho Izrael ocenil,
10 suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
a dali je podle Božího rozkazu za hrnčířovo pole.“
11 Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
Ježíš byl předveden před římského místodržitele Piláta. Ten se ho zeptal: „Tak ty jsi židovský král?“„Když tomu tak říkáš, budiž, “odpověděl mu Ježíš.
12 Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
K dalším žalobám židovské velerady se však nevyjádřil.
13 Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
„Neslyšíš, z čeho tě obviňují?“ptal se Pilát.
14 Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
Ale k jeho velkému údivu Ježíš mlčel, nehájil se.
15 A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
Bývalo zvykem, že místodržitel o velikonočních svátcích propouštěl jednoho vězně podle přání lidu.
16 To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
Tehdy právě Římané měli ve vězení zvlášť pověstného zločince jménem Barabáš.
17 Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
Když se lid toho jitra shromáždil před Pilátovým domem, zeptal se jich místodržitel: „Koho vám mám propustit – Barabáše, nebo Ježíše Krista?“
18 Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
Věděl, že Ježíše udali velekněží, protože mu záviděli jeho popularitu.
19 Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
V té chvíli dostal Pilát na soudcovském křesle vzkaz od své ženy: „Ruce pryč od toho nevinného člověka! Kvůli němu mne v noci pronásledovaly strašné sny.“
20 Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
Zástupci velerady zatím přesvědčovali lid, aby žádal svobodu pro Barabáše a pro Ježíše smrt.
21 Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
Když se Pilát znovu zeptal, koho z těch dvou má propustit, ozval se pokřik: „Barabáše!“
22 Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
„A co mám udělat s Ježíšem Kristem?“zeptal se Pilát. Dav křičel: „Ukřižuj ho!“
23 Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
Pilát ještě namítl: „Vždyť se ničeho zlého nedopustil.“Ale křik davu se stupňoval: „Na kříž! Na kříž!“
24 Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
Pilát viděl, že jeho snaha zachránit Ježíše je marná a že napětí davu roste, umyl si přede všemi ruce a řekl: „Jsem čistý od krve toho člověka. Je nevinný, odpovědnost je na vás!“
25 Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
Nato dav volal: „Jeho krev na nás i na naše děti!“
26 Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
Barabáše jim tedy propustil, Ježíše nechal zbičovat a svolil, aby byl ukřižován.
27 Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
Římští vojáci jej nejprve odvedli do vládní budovy a svolali k němu celou četu.
28 Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
Svlékli ho a přes ramena mu přehodili rudý plášť.
29 Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
Z trní upletli korunu, narazili mu ji na hlavu a do pravé ruky mu dali prut místo žezla. Pak před ním klekali a posměšně volali: „Ať žije židovský král!“
30 Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
Plivali na něj a tím prutem ho bili po hlavě.
31 Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
Když se dost pobavili, vyměnili mu zase plášť za jeho šaty a vedli ho na popraviště.
32 Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
Cestou popadli jednoho muže a přinutili ho, aby nesl Ježíšův kříž. Byl to Šimon z Kyrény.
33 Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
Došli až na pahorek zvaný Golgota – Lebka.
34 A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
Tam mu nabídli zkyslé víno s hořkou přísadou. Když ochutnal, odmítl.
35 Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
Ukřižovali ho a pak mezi sebou losovali o jeho šaty. Tím se splnilo jedno z proroctví: „Rozebrali si můj oděv, o mé šaty losovali.“
36 Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
Pak se posadili a drželi stráž.
37 Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
Nad hlavou mu připevnili nápis s označením viny: „Ježíš, král Židů.“
38 An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
Současně s ním byli po obou stranách ukřižováni dva zločinci.
39 Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
Kolemjdoucí se Ježíšovi pošklebovali
40 suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
a vysmívali: „Tak chrám jsi chtěl zbořit a za tři dny znovu postavit. Teď ukaž svou moc a zachraň sám sebe. Když jsi Boží Syn, sestup z kříže!“
41 Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
K nim se přidali i členové velerady: „Podívejte se na zachránce! Sám se zachránit neumí. Židovský král – visí na kříži! Sestup dolů a uvěříme ti.
42 “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
43 Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
Dovolával se Boha, říkal, že je Boží Syn. Ať ho tedy Bůh vysvobodí!“
44 Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
Podobná slova se ozvala i z vedlejších křížů.
45 Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
V poledne se nad celým krajem setmělo a tma trvala až do tří hodin.
46 Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
Pak Ježíš hlasitě zvolal: „Eli, Eli, lema sabachtani?“což znamená: „Bože můj, Bože můj, proč jsi mne opustil?“
47 Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
Někteří z těch, co stáli poblíž, se domnívali, že volá proroka Elijáše.
48 Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
Jeden z nich běžel pro houbu, namočil ji v tom kyselém nápoji, nastrčil na prut a podával Ježíšovi k ústům.
49 Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
Ostatní ho okřikovali: „Jen ho nech, ať vidíme, jestli mu přijde Elijáš na pomoc!“
50 Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
Potom Ježíš znovu vykřikl a zemřel.
51 A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
V tom okamžiku se v chrámu roztrhla opona, zakrývající vstup do svatyně. Tak bylo naznačeno, že úloha bohoslužeb je Kristovou obětí naplněna a končí. Země se chvěla, skály pukaly
52 Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
a hroby se otvíraly. Když pak Ježíš vstal z mrtvých, mnozí v Jeruzalémě dosvědčovali, že viděli vzkříšené z těch hrobů. Byli předzvěstí toho, že Ježíš zvítězil nad smrtí a jednou vzkřísí všechny své věrné.
53 Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
Když velitel s popravčí četou viděli zemětřesení a všechno, co se dělo, padla na ně hrůza a říkali: „On to byl opravdu Boží Syn!“
55 Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
Z povzdálí přihlíželo také mnoho žen, které přišly s Ježíšem až z Galileje a staraly se o něj a jeho učedníky.
56 A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
Mezi nimi byla i Marie Magdaléna, Marie – matka Jakuba a Josefa, a matka Jakuba a Jana Zebedeových.
57 Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
Když nastal večer, přišel jeden bohatý muž z Arimatie, jménem Josef, jeden z Ježíšových následovníků.
58 Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
Dal se ohlásit u Piláta a prosil, aby mu vydal Ježíšovo tělo. Pilát mu vyhověl.
59 Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
Josef zavinul Ježíšovo tělo do čistého plátna
60 Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
a uložil do hrobu, který si dal před nedávnem vytesat ve skále. Vchod do hrobky dal po pohřbu uzavřít těžkým balvanem. Pak odešel.
61 Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
Dvě Marie – jedna z nich Marie Magdaléna – přihlížely pohřbu.
62 Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
Druhý den v sobotu šli velekněží a farizejové k Pilátovi
63 Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
a řekli: „Pane, vzpomněli jsme si, že ten podvodník svého času řekl: ‚Třetího dne opět vstanu k životu.‘
64 Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
Dej tedy aspoň tři dny hlídat hrob, nebo přijdou jeho učedníci, ukradnou ho a pak budou lidem namlouvat, že vstal z mrtvých. A to by k tomu bludu ještě chybělo!“
65 Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
„Dobře, “řekl Pilát, „postavte tam stráž, jak myslíte.“
66 Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.
Oni šli, postavili tam stráž a dokonce zapečetili vstupní kámen.

< Mattiyu 27 >