< Mattiyu 26 >

1 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
When Jesus had ended all these discourses, He said to His disciples,
2 “Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
"You know that in two days' time the Passover comes. And the Son of Man will be delivered up to be crucified."
3 Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
Then the High Priests and Elders of the People assembled in the court of the palace of the High Priest Caiaphas,
4 suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
and consulted how to get Jesus into their power by stratagem and put Him to death.
5 Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
But they said, "Not during the Festival, lest there be a riot among the people."
6 Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
Now when Jesus was come to Bethany and was at the house of Simon the Leper,
7 wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
a woman came to Him with a jar of very costly, sweet-scented ointment, which she poured over His head as He reclined at table.
8 Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
"Why such waste?" indignantly exclaimed the disciples;
9 Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
"for this might have been sold for a considerable sum, and the money given to the poor."
10 Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
But Jesus heard it, and said to them, "Why are you vexing her? For she has done a most gracious act towards me.
11 Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
The poor you always have with you, but me you have not always.
12 Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
In pouring this ointment over me, her object was to prepare me for burial.
13 Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
In solemn truth I tell you that wherever in the whole world this Good News shall be proclaimed, this deed of hers shall be spoken of in memory of her."
14 Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
At that time one of the Twelve, the one called Judas Iscariot, went to the High Priests
15 ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
and said, "What are you willing to give me if I betray him to you?" So they weighed out to him thirty shekels,
16 Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
and from that moment he was on the look out for an opportunity to betray Him.
17 A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
On the first day of the Unleavened Bread the disciples came to Jesus with the question, "Where shall we make preparations for you to eat the Passover?"
18 Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
"Go into the city," He replied, "to a certain man, and tell him, 'The Teacher says, My time is close at hand. It is at your house that I shall keep the Passover with my disciples.'"
19 Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
The disciples did as Jesus directed them, and got the Passover ready.
20 Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
When evening came, He was at table with the twelve disciples,
21 Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
and the meal was proceeding, when Jesus said, "In solemn truth I tell you that one of you will betray me."
22 Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
Intensely grieved they began one after another to ask Him, "Can it be I, Master?"
23 Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
"The one who has dipped his fingers in the bowl with me," He answered, "is the man who will betray me.
24 Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
The Son of Man is indeed going as is written concerning Him; but alas for that man by whom the Son of Man is betrayed! It had been a happy thing for that man if he had never been born."
25 Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
Then Judas, the disciple who was betraying Him, asked, "Can it be I, Rabbi?" "It is you," He replied.
26 Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
During the meal Jesus took a Passover biscuit, blessed it and broke it. He then gave it to the disciples, saying, "Take this and eat it: it is my body."
27 Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
And He took the cup and gave thanks, and gave it to them saying, "Drink from it, all of you;
28 Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
for this is my blood which is to be poured out for many for the remission of sins--the blood which ratifies the Covenant.
29 Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
I tell you that I will never again take the produce of the vine till that day when I shall drink the new wine with you in my Father's Kingdom."
30 Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
So they sang the hymn and went out to the Mount of Olives.
31 Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
Then said Jesus, "This night all of you will stumble and fail in your fidelity to me; for it is written, 'I will strike the Shepherd, and the sheep of the flock will be scattered in all directions.'
32 Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
But after I have risen to life again I will go before you into Galilee."
33 Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
"All may stumble and fail," said Peter, "but I never will."
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
"In solemn truth I tell you," replied Jesus, "that this very night, before the cock crows, you will three times disown me."
35 Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
"Even if I must die with you," declared Peter, "I will never disown you." In like manner protested all the disciples.
36 Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
Then Jesus came with them to a place called Gethsemane. And He said to the disciples, "Sit down here, whilst I go yonder and there pray."
37 Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
And He took with Him Peter and the two sons of Zabdi. Then He began to be full of anguish and distress,
38 Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
and He said to them, "My soul is crushed with anguish to the very point of death; wait here, and keep awake with me."
39 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
Going forward a short distance He fell on His face and prayed. "My Father," He said, "if it is possible, let this cup pass away from me; nevertheless, not as I will, but as Thou willest."
40 Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
Then He came to the disciples and found them asleep, and He said to Peter, "Alas, none of you could keep awake with me for even a single hour!
41 Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
Keep awake, and pray that you may not enter into temptation: the spirit is right willing, but the body is frail."
42 Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
Again a second time He went away and prayed, saying, "My Father, if it is impossible for this cup to pass without my drinking it, Thy will be done."
43 Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
He came and again found them asleep, for they were very tired.
44 Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
So He left them, and went away once more and prayed a third time, again using the same words.
45 Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
Then He came to the disciples and said, "Sleep on and rest. See, the moment is close at hand when the Son of Man is to be betrayed into the hands of sinful men.
46 Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
Rouse yourselves. Let us be going. My betrayer is close at hand."
47 Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
He had scarcely finished speaking when Judas came--one of the Twelve--accompanied by a great crowd of men armed with swords and bludgeons, sent by the High Priests and Elders of the People.
48 To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
Now the betrayer had agreed upon a sign with them, to direct them. He had said, "The one whom I kiss is the man: lay hold of him."
49 Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
So he went straight to Jesus and said, "Peace to you, Rabbi!" And he kissed Him eagerly.
50 Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
"Friend," said Jesus, "carry out your intention." Then they came and laid their hands on Jesus and seized Him firmly.
51 Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
But one of those with Jesus drew his sword and struck the High Priest's servant, cutting off his ear.
52 Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
"Put back your sword again," said Jesus, "for all who draw the sword shall perish by the sword.
53 Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
Or do you suppose I cannot entreat my Father and He would instantly send to my help more than twelve legions of angels?
54 Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
In that case how are the Scriptures to be fulfilled which declare that thus it must be?"
55 A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
Then said Jesus to the crowds, "Have you come out as if to fight with a robber, with swords and bludgeons to apprehend me? Day after day I have been sitting teaching in the Temple, and you did not arrest me.
56 Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
But all this has taken place in order that the writings of the Prophets may be fulfilled." At this point the disciples all left Him and fled.
57 Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
But the officers who had laid hold of Jesus led Him away to Caiaphas the High Priest, at whose house the Scribes and the Elders had assembled.
58 Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
And Peter kept following Him at a distance, till he came even to the court of the High Priest's palace, where he entered and sat down among the officers to see the issue.
59 Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
Meanwhile the High Priests and the whole Sanhedrin were seeking false testimony against Jesus in order to put Him to death;
60 Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
but they could find none, although many false witnesses came forward. At length there came two
61 suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
who testified, "This man said, 'I am able to pull down the Sanctuary of God and three days afterwards to build a new one.'"
62 Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
Then the High Priest stood up and asked Him, "Have you no answer to make? What is it these men are saying in evidence against you?"
63 Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
Jesus however remained silent. Again the High Priest addressed Him. "In the name of the ever-living God," he said, "I now put you on your oath. Tell us whether you are the Christ, the Son of God."
64 Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
"I am He," replied Jesus. "But I tell you that, later on, you will see the Son of Man sitting at the right hand of Omnipotence, and coming on the clouds of the sky."
65 Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
Then the High Priest tore his robes and exclaimed, "Impious language! What further need have we of witnesses! See, you have now heard the impiety.
66 Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
What is your verdict?" "He deserves to die," they replied.
67 Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
Then they spat in His face, and struck Him--some with the fist, some with the open hand--
68 suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
while they taunted Him, saying, "Christ, prove yourself a Prophet by telling us who it was that struck you."
69 To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
Peter meanwhile was sitting outside in the court of the palace, when one of the maidservants came over to him and said, "You too were with Jesus the Galilaean."
70 Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
He denied it before them all, saying, "I do not know what you mean."
71 Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
Soon afterwards he went out and stood in the gateway, when another girl saw him, and said, addressing the people there, "This man was with Jesus the Nazarene."
72 Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
Again he denied it with an oath. "I do not know the man," he said.
73 Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
A short time afterwards the people standing there came and said to Peter, "Certainly you too are one of them, for your brogue shows it."
74 Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
Then with curses and oaths he declared, "I do not know the man." Immediately a cock crowed,
75 Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.
and Peter recollected the words of Jesus, how He had said, "Before the cock crows you will three times disown me." And he went out and wept aloud, bitterly.

< Mattiyu 26 >