< Mattiyu 25 >
1 “A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
Então o Reino dos céus será semelhante a dez virgens, que tomaram suas lâmpadas, e saíram ao encontro do noivo.
2 Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
E cinco delas eram tolas, e cinco prudentes.
3 Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
As tolas, quando tomaram as lâmpadas, não tomaram azeite consigo.
4 Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
Mas as prudentes tomaram azeite nos frascos, com as suas lâmpadas.
5 Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
O noivo demorou, por isso todas cochilaram e adormeceram.
6 “Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
Mas à meia-noite houve um grito: “Eis o noivo! Ide ao seu encontro!”.
7 “Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
Então todas aquelas virgens se levantaram, e prepararam suas lâmpadas.
8 Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
E as tolas disseram às prudentes: “Dai-nos do vosso azeite, porque as nossas lâmpadas estão se apagando”.
9 “Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
Mas as prudentes responderam: “[Não], para que não falte a nós e a vós; em vez disso, ide aos vendedores, e comprai para vós mesmas”.
10 “Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
Enquanto elas foram comprar, veio o noivo. As que estavam preparadas entraram com ele à festa do casamento, e fechou-se a porta.
11 “An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
Depois vieram também as outras virgens, dizendo: “Senhor, Senhor, abre-nos!”
12 “Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
Mas ele respondeu: “Em verdade vos digo que não vos conheço”.
13 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.
Portanto, vigiai, porque não sabeis o dia nem a hora.
14 “Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa.
Pois [é] como um homem, que partindo para fora do país, chamou seus servos, e lhes entregou os seus bens.
15 Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa.
E a um deu cinco talentos, a outro dois, e ao terceiro um, a cada um conforme a sua habilidade, e depois partiu em viagem.
16 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar.
Logo em seguida, o que havia recebido cinco talentos foi fazer negócios com eles, e ganhou outros cinco.
17 Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu.
E, semelhantemente, o que [havia recebido] dois ganhou também outros dois.
18 Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.
Mas o que tinha recebido um foi cavar a terra, e escondeu o dinheiro do seu senhor.
19 “Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su.
Muito tempo depois, o senhor daqueles servos veio fazer contas com eles.
20 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’
O que havia recebido cinco talentos chegou trazendo-lhe outros cinco talentos, e disse:”Senhor, cinco talentos me entregaste, eis que ganhei com eles outros cinco talentos”.
21 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
E o seu senhor lhe disse: “[Muito] bem, servo bom e fiel! Sobre o pouco foste fiel, sobre o muito te porei; entra na alegria do teu senhor”.
22 “Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’
E chegando-se também o que [havia recebido] dois talentos, disse: “Senhor, dois talentos me entregaste, eis que ganhei com eles outros dois talentos”.
23 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
Seu senhor lhe disse: “[Muito] bem, servo bom e fiel! Sobre o pouco foste fiel, sobre o muito te porei; entra na alegria do teu senhor”.
24 “Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba.
Mas, chegando também o que havia recebido um talento, disse: “Senhor, eu te conhecia, que és homem duro, que colhes onde não semeaste, e ajuntas onde não espalhaste;
25 Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’
E eu, atemorizado, fui e escondi o teu talento na terra; eis aqui tens o que é teu”.
26 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba?
Porém seu senhor lhe respondeu: “Servo mau e preguiçoso! Sabias que colho onde não semeei, e ajunto onde não espalhei.
27 To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.
Devias, portanto, ter depositado o meu dinheiro com os banqueiros e, quando eu voltasse, receberia o que é meu com juros.
28 “‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma.
Por isso, tirai dele o talento, e dai-o ao que tem dez talentos”.
29 Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.
Pois a todo aquele que tiver, lhe será dado, e terá em abundância; porém ao que não tiver, até o que tem lhe será tirado.
30 Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
“E lançai o servo inútil às trevas de fora (ali haverá pranto e ranger de dentes)”.
31 “Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama.
E quando o Filho do homem vier em sua glória, e todos os anjos com ele, então ele se assentará sobre o trono de sua glória.
32 Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki.
E serão ajuntadas diante dele todas as nações, e separará [as pessoas] umas das outras, assim como o pastor separa as ovelhas dos bodes.
33 Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.
E porá as ovelhas à sua direita, porém os bodes à esquerda.
34 “Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya.
Então o Rei dirá o rei aos que estiverem à sua direita: “Vinde, benditos de meu Pai! Herdai o Reino que está preparado para vós desde a fundação do mundo.
35 Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni,
Pois tive fome, e me destes de comer; tive sede, e me destes de beber; fui forasteiro, e me acolhestes;
36 da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’
[estive] nu, e me vestistes; [estive] doente, e cuidastes de mim; estive na prisão, e me visitastes”.
37 “Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha?
Então os justos lhe perguntarão: “Senhor, quando te vimos com fome, e [te] demos de comer, ou com sede, e [te] demos de beber?
38 Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura?
E quando te vimos forasteiro, e [te] acolhemos, ou nu, e te vestimos?
39 Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’
E quando te vimos doente, ou na prisão, e viemos te visitar?”
40 “Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’
E o Rei lhes responderá: “Em verdade vos digo que, todas as vezes que fizestes a um destes menores dos meus irmãos, fizestes a mim”.
41 “Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios )
Então dirá também aos que [estiverem] à esquerda: “Apartai-vos de mim, malditos, ao fogo eterno, preparado para o Diabo e os seus anjos. (aiōnios )
42 Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba,
Pois tive fome, e não me destes de comer; tive sede, e não me destes de beber.
43 da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’
Fui forasteiro, e não me acolhestes; [estive] nu, e não me vestistes; [estive] doente, e na prisão, e não me visitastes.
44 “Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’
Então também eles perguntarão: “Senhor, quando te vimos com fome, ou com sede, ou forasteiro, ou nu, ou doente, ou na prisão, e não te servimos?”
45 “Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’
Então ele lhes responderá, dizendo: “Em verdade vos digo que, todas as vezes que não fizestes a um destes menores, não fizestes a mim”.
46 “Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios )
E estes irão ao tormento eterno, porém os justos à vida eterna. (aiōnios )