< Mattiyu 25 >

1 “A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
Ngalesosikhathi umbuso wamazulu uzafananiswa lentombi ezilitshumi ezathatha izibane zazo zaphuma ukuhlangabeza umyeni.
2 Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
Njalo ezinhlanu zazo zazihlakaniphile, lezinhlanu zaziyizithutha.
3 Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
Eziyizithutha zathatha izibane zazo, kazithathanga amafutha kanye lazo;
4 Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
kodwa ezihlakaniphileyo zathatha amafutha ezitsheni kanye lezibane zazo.
5 Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
Kwathi umyeni esephuzile, zawozela zonke zalala ubuthongo.
6 “Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
Kodwa phakathi kobusuku kwamenyezwa: Khangelani, umyeni uyeza, phumani liyemhlangabeza!
7 “Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
Zasezivuka lezontombi zonke, zalungisa izibane zazo.
8 Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
Eziyizithutha zasezisithi kwezihlakaniphileyo: Sipheni okwamafutha enu, ngoba izibane zethu ziyacitsha.
9 “Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
Kodwa ezihlakaniphileyo zaphendula, zathi: Hlezi angaseneli thina lani; kodwa kungcono ukuthi lihambe liye kwabathengisayo lizithengele.
10 “Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
Kwathi zisiyathenga, weza umyeni. Ezasezilungile zasezingena laye emtshadweni, kwasekuvalwa umnyango.
11 “An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
Kwathi emva kwalokho zafika lalezontombi ezinye, zathi: Nkosi, Nkosi, sivulele!
12 “Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
Kodwa yena waphendula wathi: Ngiqinisile ngithi kini: Angilazi lina.
13 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.
Ngakho lindani, ngoba kalilwazi usuku lehola iNdodana yomuntu efika ngalo.
14 “Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa.
Ngoba kunjengomuntu owaya kwelinye ilizwe wabiza inceku zakhe, wazinika impahla zakhe;
15 Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa.
kwathi enye wayinika amathalenta amahlanu, lenye amabili, lenye lalinye, kwaba yileyo laleyo njengamandla ayo; njalo wahle wasuka.
16 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar.
Leyo eyayemukele amathalenta amahlanu yasihamba yathengiselana ngawo, yenza amanye amathalenta amahlanu.
17 Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu.
Ngokunjalo laleyo elamabili, layo yazuza amanye amabili.
18 Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.
Kodwa leyo eyayemukele elilodwa yasuka yagebha emhlabathini yayifihla imali yenkosi yayo.
19 “Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su.
Kwathi emva kwesikhathi eside inkosi yalezozinceku yafika, yasilandiselana lazo.
20 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’
Kwasekusiza eyayemukele amathalenta amahlanu yaletha amanye amathalenta amahlanu, yathi: Nkosi, wanginika amathalenta amahlanu; khangela, ngizuzile amanye amathalenta amahlanu phezu kwawo.
21 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
Inkosi yayo yasisithi kiyo: Kuhle, nceku elungileyo lethembekileyo, ubuthembekile ezintweni ezinlutshwana, ngizakubeka phezu kwezinengi; ngena entokozweni yenkosi yakho.
22 “Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’
Kwasekusiza laleyo eyayemukele amathalenta amabili yathi: Nkosi, wanginika amathalenta amabili; khangela, ngizuzile amanye amathalenta amabili phezu kwawo.
23 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
Inkosi yayo yathi kiyo: Kuhle, nceku elungileyo lethembekileyo, ubuthembekile ezintweni ezinlutshwana, ngizakubeka phezu kwezinengi; ngena entokozweni yenkosi yakho.
24 “Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba.
Kodwa kweza laleyo eyayemukele ithalenta elilodwa yathi: Nkosi, bengikwazi wena ukuthi ungumuntu olukhuni, uvuna lapho ongahlanyelanga khona, njalo ubutha lapho ongahlakazanga khona;
25 Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’
ngasengisesaba, ngasuka ngalifihla ithalenta lakho emhlabathini; khangela, ulokwakho.
26 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba?
Kodwa inkosi yayo yaphendula yathi kiyo: Nceku embi lelivila, ubusazi ukuthi ngivuna lapho engingahlanyelanga khona, njalo ngibutha lapho engingahlakazanga khona;
27 To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.
ngakho ngabe ubekile imali yami ebhanga, njalo ekufikeni kwami ngabe ngemukele okwami lenzuzo.
28 “‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma.
Ngakho mthatheleni ithalenta, lilinike yena olamathalenta alitshumi.
29 Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.
Ngoba wonke olakho uzaphiwa, uzakwengezelelwa; kodwa ongelakho uzathathelwa lalokho alakho.
30 Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
Laleyonceku engasizi lutho iphoseleni emnyameni ongaphandle; kuzakuba khona lapho ukukhala lokugedla amazinyo.
31 “Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama.
Njalo nxa isiza iNdodana yomuntu ngobukhosi bayo, lengilosi ezingcwele zonke laye, khona izahlala esihlalweni sobukhosi sodumo lwayo,
32 Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki.
kuzabuthelwa phambi kwayo izizwe zonke, njalo izabehlukanisa abanye kwabanye, njengomelusi esehlukanisa izimvu embuzini;
33 Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.
ibisibeka izimvu ngakwesokunene sayo, kodwa imbuzi ngakwesokhohlo.
34 “Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya.
Khona-ke iNkosi izakuthi kubo abangakwesokunene sayo: Wozani, lina elibusisiweyo nguBaba, lidle ilifa lombuso eliwulungiselweyo kusukela ekusekelweni komhlaba.
35 Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni,
Ngoba ngangilambile, langinika ukudla; ngangomile, langinathisa; ngangingowemzini, langemukela;
36 da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’
ngangize, langigqokisa; ngangigula, leza ukungibona; ngangisentolongweni, leza kimi.
37 “Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha?
Khona abalungileyo bezayiphendula, besithi: Nkosi, sakubona nini ulambile, njalo sakunika ukudla, kumbe womile, njalo sakunathisa?
38 Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura?
Njalo sakubona nini ungowemzini, futhi sakwemukela, kumbe uze, futhi sakugqokisa?
39 Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’
Njalo sakubona nini ugula, loba usentolongweni, njalo seza kuwe?
40 “Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’
Futhi iNkosi izaphendula ithi kubo: Ngiqinisile ngithi kini: Njengoba likwenzile komunye walaba abazalwane bami abancinyane, likwenzile kimi.
41 “Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios g166)
Ngalesosikhathi izakuthi njalo kubo abangakwesokhohlo: Sukani kimi, lina eliqalekisiweyo, liye emlilweni olaphakade, olungiselwe udiyabhola lengilosi zakhe. (aiōnios g166)
42 Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba,
Ngoba ngangilambile, kodwa kalinginikanga ukudla; ngangomile, kodwa kalinginathisanga;
43 da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’
ngangingowemzini, kodwa kalingemukelanga; ngangize, kodwa kalingigqokisanga; ngangigula, ngangisentolongweni, kodwa kalizanga ukungibona.
44 “Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’
Khona lalaba bezamphendula, besithi: Nkosi, sakubona nini ulambile, loba womile, loba ungowemzini, loba uze, loba ugula, loba usentolongweni, kodwa kasakusiza?
45 “Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’
Isizabaphendula, ithi: Ngiqinisile ngithi kini: Njengoba lingakwenzanga komunye walaba abancinyane, kalikwenzanga lakimi.
46 “Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios g166)
Lalaba bazakuya ekujezisweni okulaphakade; kodwa abalungileyo empilweni elaphakade. (aiōnios g166)

< Mattiyu 25 >