< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
Då gick Jesus sin väg utaf templet; och hans Lärjungar gingo till honom, att de skulle låta honom se templets byggning.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
Då sade Jesus till dem: Sen I icke allt detta? Sannerliga säger jag eder: Här skall icke låtas en sten på den andra, som icke blifver nederbruten.
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
Och när han satt på Oljoberget, gingo hans Lärjungar till honom afsides, och sade: Säg oss, när detta skall ske? Och hvad varder för tecken till din tillkommelse, och verldens ända? (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
Då svarade Jesus, och sade till dem: Ser till, att ingen förförer eder.
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
Ty månge skola komma i mitt Namn, och säga: Jag är Christus; och skola förföra många.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
I skolen få höra örlig, och rykte af örlig; ser till, att I blifven icke försoffade; ty allt detta måste ske, men det är icke straxt änden.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Det ena folket skall resa sig upp emot det andra, och det ena riket emot det andra; och skola blifva pestilentier, och hunger, och jordbäfning, mångastäds.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
Då skall nöden aldraförst begynnas.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Då skola de öfverantvarda eder uti tvång, och dräpa eder; och I skolen blifva hatade af all folk, för mitt Namns skull.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
Och då skola månge förargas, och inbördes den ena förråda den andra, och inbördes hata hvarannan.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
Och månge falske Propheter skola uppkomma, och förföra många.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
Och efter det ondskan får öfverhandena, varder kärleken i mångom förkolnad.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
Men den som blifver fast uti ändan, han varder salig.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
Och detta Evangelium om riket skall varda predikadt i hela verldene, till ett vittnesbörd öfver all folk; och då skall änden komma.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
När I nu fån se förödelsens styggelse, af hvilko sagdt är genom Daniel Propheten, ståndande i det helga rummet; den som läs det, han gifve akt deruppå;
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
De som då i Judiska landet äro, fly de på bergen;
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
Och den som är uppå taket, han stige icke ned, till att taga något ut af sitt hus;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
Och den som är ute på markene, gånge icke tillbaka efter sin kläder.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Men ve dem som hafvande äro, och dem som dia gifva, i den tiden.
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Men beder, att edor flykt sker icke om vintren, eller om Sabbathen.
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
Ty då skall varda en stor vedermöda, så att hon hafver icke varit sådana ifrå verldenes begynnelse och till denna tiden, ej heller varda skall.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
Och om de dagar icke vorde förstäckte, då vorde intet kött frälst; men för de utvaldas skull skola de dagar varda förstäckte.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Om någor säger då till eder: Si, här är Christus, eller der; så tror det intet.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Ty falske Christi och falske Propheter skola uppkomma, och skola göra stor tecken och under; så att, om möjeligit vore, skola ock de utvalde förförde varda.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Si, jag hafver sagt eder det framföreåt.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Derföre, om de då säga till eder: Si, han är uti öknene; går icke ut: Si, han är i kammaren; tror det icke.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
Ty såsom ljungelden går ut af öster, och synes allt intill vester; så varder ock menniskones Sons tillkommelse.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Men der som åtelen är, dit församla sig ock örnarna.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
Men straxt efter den tidsens vedermödo skall solen blifva mörk, och månen skall icke gifva sitt sken, och stjernorna skola falla af himmelen, och himlarnas krafter skola bäfva.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
Och då skall synas menniskones Sons tecken i himmelen; och då skola all slägte på jordene jämra sig, och skola se menniskones Son komma i himmelens sky, med stora kraft och härlighet.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
Och han skall utsända sina Änglar, med höga basunaröst; och de skola församla hans utvalda ifrå de fyra väder; ifrå den ena himmelens ända till den andra.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Af fikonaträt lärer en liknelse: När nu dess qvistar knoppas, och löfvet begynner springa ut, så veten I, att sommaren är hardt när;
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
Så ock, när I sen allt detta, så veter, att det är hardt för dörrene.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Sannerliga säger jag eder: Detta slägtet skall icke förgås, förrän allt detta sker.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Himmel och jord skola förgås; men min ord skola icke förgås.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
Men om den dagen och om den stundena vet ingen, icke Änglarna i himmelen, utan min Fader allena.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Men lika som det var i Noe tid, så skall ock menniskones Sons tillkommelse vara.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
Ty såsom de voro i de dagar för flodene; de åto och drucko, togo hustrur, och gåfvos mannom, intill den dagen, då Noe gick i arken;
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Och visste intet af, förr än floden kom, och tog dem allasamman bort; så skall ock menniskones Sons tillkommelse vara.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Då skola två vara ute på markene; den ene blifver upptagen, den andre blifver qvarlåten.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Två skola mala på ene qvarn; den ene blifver upptagen, den andre blifver qvarlåten.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Vaker fördenskull; ty I veten icke, hvad stund edar Herre varder kommandes.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
Men det skolen I veta att, visste husbonden, hvad stund tjufven skulle komma, förvisso vakade han och läte icke uppbryta sitt hus.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
Derföre varer I ock redo; ty, den stund I icke menen, varder menniskones Son kommandes.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Hvilken är nu en trogen och snäll tjenare, som herren hafver satt öfver sitt husfolk, att han skall gifva dem mat i rättom tid?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Salig är den tjenaren, som hans herre finner så görande, när han kommer.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Sannerliga säger jag eder, han skall sätta honom öfver alla sina ägodelar.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
Men om så är, att den onde tjenaren säger i sitt hjerta: Min herre kommer icke ännu brådt;
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
Och begynner så slå sina medtjenare; ja, äta och dricka med de druckna;
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
Så kommer dens tjenarens herre, den dag han icke väntar honom, och den stund han icke menar;
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
Och skall sönderhugga honom, och gifva honom hans lön med skrymtare. Der skall vara gråt och tandagnisslan.

< Mattiyu 24 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water