< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
In izšedši Jezus, šel je od tempeljna. Pa pristopijo učenci njegovi, da mu pokažejo zidine tempeljna.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
Jezus jim pa reče: Ne vidite li vsega tega? Resnično vam pravim: Tu ne bo ostal kamen na kamenu, kteri se ne bi podrl.
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
Ko je pa sedel na Oljskej gori, pristopijo posebéj k njemu učenci, govoreč: Povej nam, kedaj bo to? In kaj bo znamenje prihodu tvojemu in koncu sveta? (aiōn )
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
In Jezus odgovorí in jim reče: Varujte se, da vas kdo ne premoti!
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
Kajti mnogo jih bo prišlo v ime moje, govoreč: Jaz sem Kristus. In mnogo jih bodo premotili.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
Slišali boste boje in glasove o bojih. Glejte, ne ustrašite se! kajti to mora vse biti. Ali tedaj še ni konec.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Kajti vstal bo narod na narod, in kraljestvo na kraljestvo; in lakote bodo in kuge in potresi po krajih.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
Vse to je pa začetek nadlogam.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Tedaj vas bodo izročili stiski, in morili vas bodo; in sovražili vas bodo vsi narodi za voljo imena mojega.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
In tedaj se bodo pohujšali mnogi; in drug drugega bodo izdajali, in drug drugega sovražili.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
In mnogo lažnjivih prerokov bo vstalo; in premotili jih bodo veliko.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
In da se hudobnost razmnoží, omrznila bo mnogim ljubezen.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
Kdor pa pretrpí do konca, ta se bo zveličal.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
In ta evangelj se bo oznanil po vsem svetu, vsem narodom za pričo; in tedaj bo prišel konec.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
Kedar torej ugledate "gnjusobo razdevanja," za ktero je povedal prerok Danijel, da stojí na svetem prostoru: (kdor bere, naj ume!)
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
Tedaj naj tisti, kteri so v Judeji, zbežé na gore.
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
In kdor je na strehi, ne stopa naj dol, da vzeme kaj iz hiše svoje.
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
In kdor je na polji, ne vrača naj se nazaj, da vzeme plašč svoj.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Gorjé pa nosečim in doječim v tistih dnéh!
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Molite pa, da ne bo vaš beg po zimi, in ne v soboto.
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
Kajti tedaj bo velika stiska, kakoršne ni bilo od začetka sveta noter doslej, in je tudi ne bo.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
In ko se ne bi tisti dnevi prikrajšali, ne bi se nihče zveličal; ali za voljo izvoljencev se bodo prikrajšali tisti dnevi.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Če vam tedaj kdo reče: Glej, tu je Kristus, ali tam: ne verujte.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Kajti vstali bodo lažnjivi kristusi in lažnjivi preroki, in kazali bodo velika znamenja in čudeže, da bi premotili, ko bi bilo mogoče, tudi izvoljence.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Glej, povedal sem vam naprej.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Če vam torej rekó: Glej, v puščavi je! ne hodite ven: Glej, v izbah je! ne verujte.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
Kajti kakor izhaja blisk od vzhoda in se sveti do zahoda, tako bo tudi prihod sinú človečjega.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Kjerkoli namreč je mrhovina, tam se bodo zbirali orli.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
Precej po stiski tistih dnî bo pa solnce otemnelo, in mesec ne bo dajal svetlobe svoje, in zvezde bodo padale z neba, in sile nebeške se bodo pregibale.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
In tedaj se bo pokazalo na nebu znamenje sina človečjega; in tedaj bodo zajokali vsi rodovi zemlje, in videli bodo sina človečjega, da gre na nebeških oblakih z veliko močjó in slavo.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
In poslal bo angelje svoje z močnim glasom trobente, in zbrali bodo izvoljence njegove od čveterih vetrov od konca nebes do njih kraja.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Od smokve se pa naučite priliko: Kedar se veje njene omladé, in poženó listje, véste, da je blizu pomlad.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
Tako tudi vi, ko vse to ugledate, védite, da je blizu pri vratih.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Resnično vam pravim: Ne bo prešel ta rod, dokler se vse to ne zgodí.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Nebo in zemlja bosta prešla, a besede moje ne bodo prešle.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
Za tisti dan in uro pa nikdor ne vé, tudi ne angelji nebeški, nego oče moj sam.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Kakor pa v dnéh Noeta, tako bo tudi o prihodu sina človečjega.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
Kakor so namreč v dnéh pred potopom žrli in pili, ženili se in možili, do tistega dné, ko je stopil Noe v barko,
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
In niso zvedeli, dokler ni prišla voda in vseh pobrala: tako bo tudi o prihodu sina človečjega.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Tedaj bosta dva na njivi; eden se bo vzel, in eden pustil.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Dve boste mleli na mlinu; ena se bo vzela, in ena pustila.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Čujte torej! ker ne véste, obklej bo prišel gospod vaš.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
Védite pa to, da ko bi hišni gospodar vedel, o kterej straži bo prišel tat, čul bi, in ne bi dal hiše svoje podkopati.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
Za to bodite tudi vi pripravljeni; kajti sin človečji bo prišel ob uri, ko se vam ne zdí.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Kdo je torej zvesti in modri hlapec, kterega je postavil gospodar njegov nad svojimi posli, da jim daje hrano o svojem času?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blagor tistemu hlapcu, kterega bo našel gospodar njegov, kedar pride, da tako dela.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Resnično vam pravim, da ga bo postavil nad vsem svojim premoženjem.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
Če pa reče ta hudobni hlapec v srcu svojem: Gospodar moj se mudi in še ne bo prišel.
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
In začne sohlapce pretepati, in jesti in piti s pijanci:
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
Prišel bo gospodar tega hlapca, kedar ne pričakuje, in ob uri, ktere ne vé.
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
In presekal ga bo, in položil bo del njegov s hinavci: tam bo jok in škripanje z zobmí.