< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
Et Jésus sortit et s’en alla du temple; et ses disciples s’approchèrent pour lui montrer les bâtiments du temple.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
Et lui, répondant, leur dit: Ne voyez-vous pas toutes ces choses? En vérité, je vous dis: Il ne sera point laissé ici pierre sur pierre qui ne soit jetée à bas.
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
Et comme il était assis sur la montagne des Oliviers, les disciples vinrent à lui en particulier, disant: Dis-nous quand ces choses auront lieu, et quel sera le signe de ta venue et de la consommation du siècle. (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
Et Jésus, répondant, leur dit: Prenez garde que personne ne vous séduise;
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
car plusieurs viendront en mon nom, disant: Moi, je suis le Christ; et ils en séduiront plusieurs.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
Et vous entendrez parler de guerres et de bruits de guerres; prenez garde que vous ne soyez troublés, car il faut que tout arrive; mais la fin n’est pas encore.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Car nation s’élèvera contre nation, et royaume contre royaume; et il y aura des famines, et des pestes, et des tremblements de terre en divers lieux.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
Mais toutes ces choses sont un commencement de douleurs.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Alors ils vous livreront pour être affligés, et ils vous feront mourir; et vous serez haïs de toutes les nations à cause de mon nom.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
Et alors plusieurs seront scandalisés, et se livreront l’un l’autre, et se haïront l’un l’autre;
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
et plusieurs faux prophètes s’élèveront et en séduiront plusieurs:
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
et parce que l’iniquité prévaudra, l’amour de plusieurs sera refroidi;
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
mais celui qui persévérera jusqu’à la fin, celui-là sera sauvé.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
Et cet évangile du royaume sera prêché dans la terre habitée tout entière, en témoignage à toutes les nations; et alors viendra la fin.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
Quand donc vous verrez l’abomination de la désolation, dont il a été parlé par Daniel le prophète, établie dans [le] lieu saint (que celui qui lit comprenne),
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
alors que ceux qui sont en Judée s’enfuient dans les montagnes;
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
que celui qui est sur le toit ne descende pas pour emporter ses effets hors de sa maison;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
et que celui qui est aux champs ne retourne pas en arrière pour emporter son vêtement.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Mais malheur à celles qui sont enceintes et à celles qui allaitent en ces jours-là!
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Et priez que votre fuite n’ait pas lieu en hiver, ni un jour de sabbat;
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
car alors il y aura une grande tribulation, telle qu’il n’y en a point eu depuis le commencement du monde jusqu’à maintenant, et qu’il n’y en aura jamais.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
Et si ces jours-là n’avaient été abrégés, nulle chair n’aurait été sauvée; mais, à cause des élus, ces jours-là seront abrégés.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Alors, si quelqu’un vous dit: Voici, le Christ est ici, ou: Il est là, ne le croyez pas.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Car il s’élèvera de faux christs et de faux prophètes; et ils montreront de grands signes et des prodiges, de manière à séduire, si possible, même les élus.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Voici, je vous l’ai dit à l’avance.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Si donc on vous dit: Voici, il est au désert, ne sortez pas; voici, il est dans les chambres intérieures, ne le croyez pas.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
Car comme l’éclair sort de l’orient et apparaît jusqu’à l’occident, ainsi sera la venue du fils de l’homme.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Car, où que soit le corps mort, là s’assembleront les aigles.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
Et aussitôt après la tribulation de ces jours-là, le soleil sera obscurci, et la lune ne donnera pas sa lumière, et les étoiles tomberont du ciel, et les puissances des cieux seront ébranlées.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
Et alors paraîtra le signe du fils de l’homme dans le ciel: et alors toutes les tribus de la terre se lamenteront et verront le fils de l’homme venant sur les nuées du ciel, avec puissance et une grande gloire.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
Et il enverra ses anges avec un grand son de trompette; et ils rassembleront ses élus des quatre vents, depuis l’un des bouts du ciel jusqu’à l’autre bout.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Mais apprenez du figuier la parabole [qu’il vous offre]: Quand déjà son rameau est tendre et qu’il pousse des feuilles, vous connaissez que l’été est proche.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
De même aussi vous, quand vous verrez toutes ces choses, sachez que cela est proche, à la porte.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous dis: Cette génération ne passera point que toutes ces choses ne soient arrivées.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
Mais, quant à ce jour-là et à l’heure, personne n’en a connaissance, pas même les anges des cieux, si ce n’est mon Père seul.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Mais comme ont été les jours de Noé, ainsi sera aussi la venue du fils de l’homme.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
Car, comme dans les jours avant le déluge on mangeait et on buvait, on se mariait et on donnait en mariage, jusqu’au jour où Noé entra dans l’arche,
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
et ils ne connurent rien, jusqu’à ce que le déluge vint et les emporta tous, ainsi sera aussi la venue du fils de l’homme.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Alors deux hommes seront au champ, l’un sera pris et l’autre laissé;
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
deux femmes moudront à la meule, l’une sera prise et l’autre laissée.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Veillez donc; car vous ne savez pas à quelle heure votre Seigneur vient.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
Mais sachez ceci, que si le maître de la maison avait su à quelle veille le voleur devait venir, il aurait veillé, et n’aurait pas laissé percer sa maison.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
C’est pourquoi, vous aussi, soyez prêts; car, à l’heure que vous ne pensez pas, le fils de l’homme vient.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Qui donc est l’esclave fidèle et prudent, que son maître a établi sur les domestiques de sa maison pour leur donner leur nourriture au temps convenable?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Bienheureux est cet esclave-là que son maître, lorsqu’il viendra, trouvera faisant ainsi.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
En vérité, je vous dis qu’il l’établira sur tous ses biens.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
Mais si ce méchant esclave-là dit en son cœur: Mon maître tarde à venir,
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
et qu’il se mette à battre ceux qui sont esclaves avec lui, et qu’il mange et boive avec les ivrognes,
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
le maître de cet esclave-là viendra en un jour qu’il n’attend pas, et à une heure qu’il ne sait pas,
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
et il le coupera en deux et lui donnera sa part avec les hypocrites: là seront les pleurs et les grincements de dents.

< Mattiyu 24 >