< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
And having gone forth, Jesus departed from the temple, and his disciples came near to show him the buildings of the temple,
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
and Jesus said to them, 'Do ye not see all these? verily I say to you, There may not be left here a stone upon a stone, that shall not be thrown down.'
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
And when he is sitting on the mount of the Olives, the disciples came near to him by himself, saying, 'Tell us, when shall these be? and what [is] the sign of thy presence, and of the full end of the age?' (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
And Jesus answering said to them, 'Take heed that no one may lead you astray,
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
for many shall come in my name, saying, I am the Christ, and they shall lead many astray,
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
and ye shall begin to hear of wars, and reports of wars; see, be not troubled, for it behoveth all [these] to come to pass, but the end is not yet.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
'For nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom, and there shall be famines, and pestilences, and earthquakes, in divers places;
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
and all these [are] the beginning of sorrows;
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
then they shall deliver you up to tribulation, and shall kill you, and ye shall be hated by all the nations because of my name;
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
and then shall many be stumbled, and they shall deliver up one another, and shall hate one another.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
'And many false prophets shall arise, and shall lead many astray;
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
and because of the abounding of the lawlessness, the love of the many shall become cold;
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
but he who did endure to the end, he shall be saved;
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
and this good news of the reign shall be proclaimed in all the world, for a testimony to all the nations; and then shall the end arrive.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
'Whenever, therefore, ye may see the abomination of the desolation, that was spoken of through Daniel the prophet, standing in the holy place (whoever is reading let him observe)
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
then those in Judea — let them flee to the mounts;
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
he on the house-top — let him not come down to take up any thing out of his house;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
and he in the field — let him not turn back to take his garments.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
'And woe to those with child, and to those giving suck in those days;
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
and pray ye that your flight may not be in winter, nor on a sabbath;
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
for there shall be then great tribulation, such as was not from the beginning of the world till now, no, nor may be.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
And if those days were not shortened, no flesh would have been saved; but because of the chosen, shall those days be shortened.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
'Then if any one may say to you, Lo, here [is] the Christ! or here! ye may not believe;
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
for there shall arise false Christs, and false prophets, and they shall give great signs and wonders, so as to lead astray, if possible, also the chosen.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Lo, I did tell you beforehand.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
'If therefore they may say to you, Lo, in the wilderness he is, ye may not go forth; lo, in the inner chambers, ye may not believe;
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
for as the lightning doth come forth from the east, and doth appear unto the west, so shall be also the presence of the Son of Man;
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
for wherever the carcase may be, there shall the eagles be gathered together.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
'And immediately after the tribulation of those days, the sun shall be darkened, and the moon shall not give her light, and the stars shall fall from the heaven, and the powers of the heavens shall be shaken;
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
and then shall appear the sign of the Son of Man in the heaven; and then shall all the tribes of the earth smite the breast, and they shall see the Son of Man coming upon the clouds of the heaven, with power and much glory;
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
and he shall send his messengers with a great sound of a trumpet, and they shall gather together his chosen from the four winds, from the ends of the heavens unto the ends thereof.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
'And from the fig-tree learn ye the simile: When already its branch may have become tender, and the leaves it may put forth, ye know that summer [is] nigh,
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
so also ye, when ye may see all these, ye know that it is nigh — at the doors.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Verily I say to you, this generation may not pass away till all these may come to pass.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
The heaven and the earth shall pass away, but my words shall not pass away.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
'And concerning that day and the hour no one hath known — not even the messengers of the heavens — except my Father only;
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
and as the days of Noah — so shall be also the presence of the Son of Man;
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
for as they were, in the days before the flood, eating, and drinking, marrying, and giving in marriage, till the day Noah entered into the ark,
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
and they did not know till the flood came and took all away; so shall be also the presence of the Son of Man.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Then two men shall be in the field, the one is received, and the one is left;
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
two women shall be grinding in the mill, one is received, and one is left.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
'Watch ye therefore, because ye have not known in what hour your Lord doth come;
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
and this know, that if the master of the house had known in what watch the thief doth come, he had watched, and not suffered his house to be broken through;
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
because of this also ye, become ye ready, because in what hour ye do not think, the Son of Man doth come.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
'Who, then, is the servant, faithful and wise, whom his lord did set over his household, to give them the nourishment in season?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Happy that servant, whom his lord, having come, shall find doing so;
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
verily I say to you, that over all his substance he will set him.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
'And, if that evil servant may say in his heart, My Lord doth delay to come,
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
and may begin to beat the fellow-servants, and to eat and to drink with the drunken,
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
the lord of that servant will arrive in a day when he doth not expect, and in an hour of which he doth not know,
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
and will cut him off, and his portion with the hypocrites will appoint; there shall be the weeping and the gnashing of the teeth.

< Mattiyu 24 >