< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
And Jhesus wente out of the temple; and his disciplis camen to hym, to schewe hym the bildyngis of the temple.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
But he answeride, and seide to hem, Seen ye alle these thingis? Treuli Y seie to you, a stoon schal not be left here on a stoon, that ne it schal be destried.
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
And whanne he satte on the hille of Olyuete, hise disciplis camen to hym priueli, and seiden, Seie vs, whanne these thingis schulen be, and what token of thi comyng, and of the ending of the world. (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
And Jhesus answeride, and seide to hem, Loke ye, that no man disseyue you.
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
For many schulen come in my name, and schulen seie, Y am Crist; and thei schulen disseyue manye.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
For ye schulen here batels, and opyniouns of batels; se ye that ye be not disturblid; for it byhoueth these thingis to be don, but not yit is the ende.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Folk schal rise togidere ayens folc, and rewme ayens rewme, and pestilences, and hungris, and the erthemouyngis schulen be bi placis;
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
and alle these ben bigynnyngis of sorewes.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Thanne men schulen bitake you in to tribulacion, and schulen sle you, and ye schulen be in hate to alle folk for my name.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
And thanne many schulen be sclaundrid, and bitraye ech other, and thei schulen hate ech other.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
And many false prophetis schulen rise, and disseyue manye.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
And for wickidnesse schal `be plenteuouse, the charite of manye schal wexe coold;
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
but he that schal dwelle stable in to the ende, schal be saaf.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
And this gospel of the kyngdom schal be prechid in al the world, in witnessyng to al folc;
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
and thanne the ende schal come. Therfor whanne ye se the abhomynacioun of discomfort, that is seid of Danyel, the prophete, stondynge in the hooli place; he that redith, vndirstonde he;
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
thanne thei that ben in Judee, fle to the mounteyns; and he that is in the hous roof,
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
come not doun to take ony thing of his hous; and he that is in the feeld,
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
turne not ayen to take his coote.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
But wo to hem that ben with child, and nurischen in tho daies.
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Preye ye, that youre fleyng be not maad in wynter, or in the saboth.
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
For thanne schal be greet tribulacioun, what maner `was not fro the bigynnyng of the world to now, nether schal be maad.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
And but tho daies hadden be abreggide, ech flesch schulde not be maad saaf; but tho daies schulen be maad schort, for the chosun men.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Thanne if ony man seie to you, Lo! here is Crist, or there, nyle ye bileue.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For false Cristis and false prophetis schulen rise, and thei schulen yyue grete tokenes and wondrys; so that also the chosun be led in to erroure, if it may be done.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Lo! Y haue bifor seid to you.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Therfor if thei seie to you, Lo! he is in desert, nyle ye go out; lo! in priuey placis, nyle ye trowe.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
For as leit goith out fro the eest, and apperith in to the weste, so schal be also the coming of mannus sone.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Where euer the bodi schal be, also the eglis schulen be gaderid thidur.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
And anoon after the tribulacioun of tho daies, the sunne schal be maad derk, and the moone schal not yyue hir liyt, and the sterris schulen falle fro heuene, and the vertues of heuenes schulen be moued.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
And thanne the tokene of mannus sone schal appere in heuene, and thanne alle kynredis of the erthe schulen weile; and thei schulen see mannus sone comynge in the cloudis of heuene, with miche vertu and maieste.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
And he schal sende hise aungels with a trumpe, and a greet vois; and thei schulen gedere hise chosun fro foure wyndis, fro the hiyest thingis of heuenes to the endis of hem.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
And lerne ye the parable of a fige tre. Whanne his braunche is now tendir, and the leeues ben sprongun, ye witen that somer is nyy;
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
`so and ye whanne ye seen alle these thingis, wite ye that it is nyy, in the yatis.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Treuli Y seie to you, for this generacioun schal not passe, til alle thingis be don;
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
heuene and erthe schulen passe, but my wordis schulen not passe.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
But of thilke dai and our no man wote, nethir aungels of heuenes, but the fadir aloone.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
But as it was in the daies of Noe, so schal be the comyng of mannus sone.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
For as in the daies bifore the greet flood, thei weren etynge and drynkynge, weddynge and takynge to weddyng, to that dai, that Noe entride in to the schippe;
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
and thei knewen not, til the greet flood cam, and took alle men, so schal be the comyng of mannus sone.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Thanne tweyne schulen be in o feeld, oon schal be takun, and another left;
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
twey wymmen schulen be gryndynge in o queerne, oon schal be takun, and `the tother left; tweyn in a bedde, `the toon schal be takun, and the tother left.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Therfor wake ye, for ye witen not in what our the Lord schal come.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
But wite ye this, that if the hosebonde man wiste in what our the thefe were to come, certis he wolde wake, and suffre not his hous to be vndurmyned.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
And therfor be ye redi, for in what our ye gessen not, mannus sone schal come.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Who gessist thou is a trewe seruaunt and prudent, whom his lord ordeyned on his meynee, to yyue hem mete in tyme?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blessed is that seruaunt, whom `his lord, whanne he schal come, schal fynde so doynge.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Treuli Y seye to you, for on alle his goodis he schal ordeyne hym.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
But if thilke yuel seruaunt seie in his herte, My lord tarieth to come,
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
and bigynneth to smyte hise euen seruauntis, and ete, and drynke with drunken men;
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
the lord of that seruaunt schal come in the dai which he hopith not, and in the our that he knowith not,
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
and schal departe hym, and putte his part with ypocritis; there schal be wepyng, and gryntyng of teeth.

< Mattiyu 24 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water