< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
And as Jesus went out, and was departing from the temple, his disciples came to observe to Him the magnificent buildings.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
But Jesus said unto them, Do ye see all these things? Verily I tell you, there shall not be left here one stone upon another, that shall not be demolished.
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
And when He was got to the mount of olives, the disciples came to Him in private and said, Tell us when these things shall be, and what shall be the sign of thy coming, and of the end of the world. (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
And Jesus answered them, See that no one deceive you:
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
for many shall come in my name saying, I am the Christ, and shall deceive many.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
And ye shall hear of wars and rumors of wars, but be not troubled; for all these must indeed come to pass, but the end is not yet.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
For nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom; and there shall be famines, and pestilences, and earthquakes in several places:
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
all which are but the beginning of sorrows.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Then shall they afflict you, and kill you; and ye shall be hated by all nations for my name:
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
and then will many take offense, and betray one another, and hate one another: and many false prophets will rise up and deceive many:
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
and because iniquity shall abound,
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
the love of many will grow cold.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
But he that endures to the end, shall be saved:
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
and this gospel of the kingdom of heaven shall be preached in all the world, for a testimony to all the nations; and then shall the end come.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
When therefore ye shall see the desolating abomination, spoken of by Daniel the prophet, standing at the holy place, (let him, that readeth, attend) then let those in Judea flee to the mountains:
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
let not him that is at the top of the house come down into it,
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
to take any thing out of his house;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
nor let him that is in the field return back to take his clothes.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
But wo to them that are with child, and to them that give suck, in those days.
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Pray that your flight be not in the winter, nor on the sabbath:
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
for there shall be then great affliction, such as has not been from the beginning of the world unto this time, no, nor ever shall be.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
And unless those days be shortened, no one would be saved; but for the sake of the elect those days shall be shortened.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Then if any shall say to you, Behold here is the Messiah, or there; believe it not:
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
for there shall rise up false Christs, and false prophets, who shall shew great signs and prodigies, so as to deceive, if possible, even the elect.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Lo, I have told you before-hand: and therefore if they say to you,
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Behold, he is in the desert, go not out: behold, he is the secret chambers, believe them not:
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
for as the lightning cometh from the east, and flashes in an instant even to the west, so shall be the coming of the Son of man.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
For wheresoever the carcase is, there will the eagles be gathered together.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
And immediately after the affliction of those days, the fun shall be darkened, and the moon shall not give it's light, and the stars shall fall from heaven, and the powers of the heavens shall be shaken:
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
and then shall appear the sign of the Son of man in heaven, and then shall all the tribes of the land mourn, and they shall see the Son of man coming as on the clouds of heaven with power and great glory:
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
and He will send forth his messengers with a trumpet of a loud voice, and they shall gather his elect from the four winds, from one end of heaven to the other.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Now learn a parable from the fig-tree: when it's branch is tender and bringeth forth leaves, ye know that summer is nigh;
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
so ye also, when ye shall see all these things, know that it is near even at the doors.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Verily I tell you, this generation shall not pass away, till all these be fulfilled.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Heaven and earth shall pass away, but my words shall not pass away.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
But of THAT day and hour knoweth no one, not even the angels of heaven, but my Father only:
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
for as the days of Noah were, so shall be also the coming of the Son of man;
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
for as in the days before the flood they were eating and drinking, marrying and giving in marriage, till the day that Noah entered into the ark,
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
and knew not of it till the deluge came and took them all away; so shall be also the coming of the Son of man.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Then there shall be two in the field, the one shall be taken and the other left:
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
and two women grinding at the mill, one taken and one left.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Watch therefore, for ye know not at what hour your Lord cometh:
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
but this ye know, that if the master of the house had known at what hour the thief would come, he would have watched, and would not have suffered his house to be broke open: therefore be ye also ready;
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
for the Son of man cometh at a time that ye think not of.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Who then is the faithful and prudent servant, whom his lord hath set over his family to give them food in due season?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
blessed is that servant, whom his lord when he cometh shall find so employed:
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
verily I tell you, that he will set him over his whole estate.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
But if that servant be wicked and say in his heart, my master delayeth his coming,
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
and begin to beat his fellow-servants, and to revel with drunkards:
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
the lord of that servant will come in a day when he doth not expect him, and in an hour which he knows not,
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
and will cut him asunder, and appoint him his portion with hypocrites: where there will be weeping and gnashing of teeth.

< Mattiyu 24 >