< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
Jesus had left the Temple and was going on His way, when His disciples came and called His attention to the Temple buildings.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
"You see all these?" He replied; "in solemn truth I tell you that there will not be left here one stone upon another that will not be pulled down."
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
Afterwards He was on the Mount of Olives and was seated there when the disciples came to Him, apart from the others, and said, "Tell us when this will be; and what will be the sign of your Coming and of the Close of the Age?" (aiōn )
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
"Take care that no one misleads you," answered Jesus;
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
"for many will come assuming my name and saying 'I am the Christ;' and they will mislead many.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
And before long you will hear of wars and rumours of wars. Do not be alarmed, for such things must be; but the End is not yet.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
For nation will rise in arms against nation, kingdom against kingdom, and there will be famines and earthquakes in various places;
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
but all these miseries are but like the early pains of childbirth.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
"At that time they will deliver you up to punishment and will put you to death; and you will be objects of hatred to all the nations because you are called by my name.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
Then will many stumble and fall, and they will betray one another and hate one another.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
Many false prophets will rise up and lead multitudes astray;
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
and because of the prevalent disregard of God's law the love of the great majority will grow cold;
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
but those who stand firm to the End shall be saved.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
And this Good News of the Kingdom shall be proclaimed throughout the whole world to set the evidence before all the Gentiles; and then the End will come.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
"When you have seen (to use the language of the Prophet Daniel) the 'Abomination of Desolation', standing in the Holy Place" --let the reader observe those words--
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
"then let those who are in Judaea escape to the hills;
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
let him who is on the roof not go down to fetch what is in his house;
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
nor let him who is outside the city stay to pick up his outer garment.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
And alas for the women who at that time are with child or have infants!
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
"But pray that your flight may not be in winter, nor on the Sabbath;
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
for it will be a time of great suffering, such as never has been from the beginning of the world till now, and assuredly never will be again.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
And if those days had not been cut short, no one would escape; but for the sake of God's own People those days will be cut short.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
"If at that time any one should say to you, 'See, here is the Christ!' or 'Here!' give no credence to it.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For there will rise up false Christs and false prophets, displaying wonderful signs and prodigies, so as to deceive, were it possible, even God's own People.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Remember, I have forewarned you.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
If therefore they should say to you, 'See, He is in the Desert!' do not go out there: or 'See, He is indoors in the room!' do not believe it.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
For just as the lightning flashes in the east and is seen to the very west, so will be the Coming of the Son of Man.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Wherever the dead body is, there will the vultures flock together.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
"But immediately after those times of distress the sun will be darkened, the moon will not shed her light, the stars will fall from the firmament, and the forces which control the heavens will be disordered and disturbed.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
Then will appear the Sign of the Son of Man in the sky; and then will all the nations of the earth lament, when they see the Son of Man coming on the clouds of the sky with great power and glory.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
And He will send out His angels with a loud trumpet-blast, and they will bring together His own People to Him from north, south, east and west--from one extremity of the world to the other.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
"Now learn from the fig-tree the lesson it teaches. As soon as its branches have now become soft and it is bursting into leaf, you all know that summer is near.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
So you also, when you see all these signs, may be sure that He is near--at your very door.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
I tell you in solemn truth that the present generation will certainly not pass away without all these things having first taken place.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Earth and sky will pass away, but it is certain that my words will not pass away.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
"But as to that day and the exact time no one knows--not even the angels of heaven, nor the Son, but the Father alone.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
'For as it was in the time of Noah, so it will be at the Coming of the Son of Man.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
At that time, before the Deluge, men were busy eating and drinking, taking wives or giving them, up to the very day when Noah entered the Ark,
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
nor did they realise any danger till the Deluge came and swept them all away; so will it be at the Coming of the Son of Man.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Then will two men be in the open country: one will be taken away, and one left behind.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Two women will be grinding at the mill: one will be taken away, and one left behind.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Be on the alert therefore, for you do not know the day on which your Lord is coming.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
But of this be assured, that if the master of the house had known the hour at which the robber was coming, he would have kept awake, and not have allowed his house to be broken into.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
Therefore you also must be ready; for it is at a time when you do not expect Him that the Son of Man will come.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
"Who therefore is the loyal and intelligent servant to whom his master has entrusted the control of his household to give them their rations at the appointed time?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blessed is that servant whom his master when he comes shall find so doing!
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
In solemn truth I tell you that he will give him the management of all his wealth.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
But if the man, being a bad servant, should say in his heart, 'My master is a long time in coming,'
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
and should begin to beat his fellow servants, while he eats and drinks with drunkards;
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
the master of that servant will arrive on a day when he is not expecting him and at an hour of which he has not been informed;
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
he will treat him with the utmost severity and assign him a place among the hypocrites: there will be the weeping and the gnashing of teeth.