< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
And Jesus departed from the temple and went away. And his disciples approached him, so as to show him the buildings of the temple.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
But he said to them in response: “Do you see all these things? Amen I say to you, there shall not remain here stone upon stone, which is not torn down.”
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
Then, when he was seated at the Mount of Olives, the disciples drew near to him privately, saying: “Tell us, when will these things be? And what will be the sign of your advent and of the consummation of the age?” (aiōn )
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
And answering, Jesus said to them: “Pay attention, lest someone lead you astray.
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
For many will come in my name saying, ‘I am the Christ.’ And they will lead many astray.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
For you will hear of battles and rumors of battles. Take care not to be disturbed. For these things must be, but the end is not so soon.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom. And there will be pestilences, and famines, and earthquakes in places.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
But all these things are just the beginning of the sorrows.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Then they will hand you over to tribulation, and they will kill you. And you will be hated by all nations for the sake of my name.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
And then many will be led into sin, and will betray one another, and will have hatred for one another.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
And many false prophets will arise, and they will lead many astray.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
And because iniquity has abounded, the charity of many will grow cold.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
But whoever will have persevered until the end, the same shall be saved.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
And this Gospel of the kingdom shall be preached throughout the entire world, as a testimony to all nations. And then the consummation will occur.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
Therefore, when you will have seen the abomination of desolation, which was spoken of by the prophet Daniel, standing in the holy place, may he who reads understand,
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
then those who are in Judea, let them flee to the mountains.
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
And whoever is on the roof, let him not descend to take anything from his house.
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
And whoever is in the field, let him not turn back to take his tunic.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
So then, woe to those who are pregnant or nursing in those days.
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
But pray that your flight may not be in winter, or on the Sabbath.
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
For then there will be a great tribulation, such as has not been from the beginning of the world until the present, and such as will not be.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
And unless those days had been shortened, no flesh would be saved. But for the sake of the elect, those days shall be shortened.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Then if anyone will have said to you, ‘Behold, here is the Christ,’ or ‘he is there,’ do not be willing to believe it.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For there will arise false Christs and false prophets. And they will produce great signs and wonders, so much so as to lead into error even the elect (if this could be).
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Behold, I have warned you beforehand.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Therefore, if they will have said to you, ‘Behold, he is in the desert,’ do not choose to go out, or, ‘Behold, he is in the inner rooms,’ do not be willing to believe it.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
For just as lightning goes out from the east, and appears even in the west, so shall it be also at the advent of the Son of man.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Wherever the body shall be, there also will the eagles be gathered together.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
And immediately after the tribulation of those days, the sun will be darkened, and the moon will not give its light, and the stars will fall from heaven, and the powers of the heavens will be shaken.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
And then the sign of the Son of man shall appear in heaven. And then all tribes of the earth shall mourn. And they shall see the Son of man coming on the clouds of heaven, with great power and majesty.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
And he shall send out his Angels with a trumpet and a great voice. And they shall gather together his elect from the four winds, from the heights of the heavens, even to their furthest limits.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
So, from the fig tree learn a parable. When its branch has now become tender and the leaves have sprung forth, you know that summer is near.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
So also, when you will have seen all these things, know that it is near, even at the threshold.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Amen I say to you, that this lineage shall not pass away, until all these things have been done.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Heaven and earth shall pass away, but my words shall not pass away.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
But concerning that day and hour, no one knows, not even the Angels of the heavens, but only the Father.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
And just as in the days of Noah, so also will be the advent of the Son of man.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
For it will be just as it was in the days before the flood: eating and drinking, marrying and being given in marriage, even until that day when Noah entered into the ark.
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
And they did not realize it, until the flood came and took them all away. So also will the advent of the Son of man be.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Then two men will be in a field: one will be taken up, and one will be left behind.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Two women will be grinding at a millstone: one will be taken up, and one will be left behind.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Therefore, be vigilant. For you do not know at what hour your Lord will return.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
But know this: if only the father of the family knew at what hour the thief would arrive, he would certainly keep vigil and not permit his house to be broken into.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
For this reason, you also must be prepared, for you do not know at what hour the Son of man will return.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Consider this: who is a faithful and prudent servant, who has been appointed by his lord over his family, to give them their portion in due time?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blessed is that servant, if, when his lord has arrived, he shall find him doing so.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Amen I say to you, he shall appoint him over all of his goods.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
But if that evil servant has said in his heart, ‘My lord has been delayed in returning,’
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
and so, he begins to strike his fellow servants, and he eats and drinks with the inebriated:
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
then the lord of that servant will arrive on a day that he does not expect, and at an hour that he does not know.
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
And he shall separate him, and he shall place his portion with the hypocrites, where there shall be weeping and gnashing of teeth.”