< Mattiyu 24 >
1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
As Jesus left the temple and was walking away, His disciples came up to Him to point out its buildings.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
“Do you see all these things?” He replied. “Truly I tell you, not one stone here will be left on another; every one will be thrown down.”
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
While Jesus was sitting on the Mount of Olives, the disciples came to Him privately. “Tell us,” they said, “when will these things happen, and what will be the sign of Your coming and of the end of the age?” (aiōn )
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
Jesus answered, “See to it that no one deceives you.
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
For many will come in My name, claiming, ‘I am the Christ,’ and will deceive many.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
You will hear of wars and rumors of wars, but see to it that you are not alarmed. These things must happen, but the end is still to come.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom. There will be famines and earthquakes in various places.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
All these are the beginning of birth pains.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Then they will deliver you over to be persecuted and killed, and you will be hated by all nations because of My name.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
At that time many will fall away and will betray and hate one another,
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
and many false prophets will arise and mislead many.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
Because of the multiplication of wickedness, the love of most will grow cold.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
But the one who perseveres to the end will be saved.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
And this gospel of the kingdom will be preached in all the world as a testimony to all nations, and then the end will come.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
So when you see standing in the holy place ‘the abomination of desolation,’ described by the prophet Daniel (let the reader understand),
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
then let those who are in Judea flee to the mountains.
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
Let no one on the housetop come down to retrieve anything from his house.
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
And let no one in the field return for his cloak.
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
How miserable those days will be for pregnant and nursing mothers!
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Pray that your flight will not occur in the winter or on the Sabbath.
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
For at that time there will be great tribulation, unmatched from the beginning of the world until now, and never to be seen again.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
If those days had not been cut short, nobody would be saved. But for the sake of the elect, those days will be cut short.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
At that time, if anyone says to you, ‘Look, here is the Christ!’ or ‘There He is!’ do not believe it.
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For false Christs and false prophets will appear and perform great signs and wonders that would deceive even the elect, if that were possible.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
See, I have told you in advance.
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
So if they tell you, ‘There He is in the wilderness,’ do not go out; or, ‘Here He is in the inner rooms,’ do not believe it.
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
For just as the lightning comes from the east and flashes as far as the west, so will be the coming of the Son of Man.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Wherever there is a carcass, there the vultures will gather.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
Immediately after the tribulation of those days: ‘The sun will be darkened, and the moon will not give its light; the stars will fall from the sky, and the powers of the heavens will be shaken.’
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
At that time the sign of the Son of Man will appear in heaven, and all the tribes of the earth will mourn. They will see the Son of Man coming on the clouds of heaven, with power and great glory.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
And He will send out His angels with a loud trumpet call, and they will gather His elect from the four winds, from one end of the heavens to the other.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Now learn this lesson from the fig tree: As soon as its branches become tender and sprout leaves, you know that summer is near.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
So also, when you see all these things, you will know that He is near, right at the door.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Truly I tell you, this generation will not pass away until all these things have happened.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Heaven and earth will pass away, but My words will never pass away.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
No one knows about that day or hour, not even the angels in heaven, nor the Son, but only the Father.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
As it was in the days of Noah, so will it be at the coming of the Son of Man.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
For in the days before the flood, people were eating and drinking, marrying and giving in marriage, up to the day Noah entered the ark.
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
And they were oblivious, until the flood came and swept them all away. So will it be at the coming of the Son of Man.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Two men will be in the field: one will be taken and the other left.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Two women will be grinding at the mill: one will be taken and the other left.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Therefore keep watch, because you do not know the day on which your Lord will come.
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
But understand this: If the homeowner had known in which watch of the night the thief was coming, he would have kept watch and would not have let his house be broken into.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
For this reason, you also must be ready, because the Son of Man will come at an hour you do not expect.
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Who then is the faithful and wise servant, whom the master has put in charge of his household, to give the others their food at the proper time?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Blessed is that servant whose master finds him doing so when he returns.
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Truly I tell you, he will put him in charge of all his possessions.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
But suppose that servant is wicked and says in his heart, ‘My master will be away a long time.’
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
And he begins to beat his fellow servants and to eat and drink with drunkards.
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
The master of that servant will come on a day he does not expect and at an hour he does not anticipate.
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
Then he will cut him to pieces and assign him a place with the hypocrites, where there will be weeping and gnashing of teeth.