< Mattiyu 23 >
1 Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
Then Jesus speaking to the crowds and to his disciples, said:
2 “Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
“The teachers of the Law and the Pharisees now occupy the chair of Moses.
3 Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
Therefore practice and lay to heart everything that they tell preach but do not practice.
4 Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
While they make up heavy loads and pile them on other men’s shoulder’s they decline, themselves, to lift a finger to move them.
5 “Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
All their actions are done to attract attention. They widen their phylacteries, and increase the size of their tassels,
6 suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
and like to have the place of honour at dinner, and the best seats in the Synagogues,
7 suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
and to be greeted in the markets with respect, and to be called ‘Rabbi’ for everybody.
8 “Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
But do not allow yourselves to be called ‘Rabbi,’ for you have only one Teacher, and you yourselves are all Brothers.
9 Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
And do not call any one on the earth your ‘Father,’ for your have only one Father, the heavenly Father.
10 Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
Nor must you allow yourselves to be called ‘Leaders,’ for you have only one Leader, the Christ.
11 Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
The man who would be the greatest among you must be your servant.
12 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
Whoever shall exalt himself will be humbled, and whoever shall humble himself will be exalted.
13 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
But alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You turn the key of the Kingdom of Heaven in men’s faces. For you do not go in yourselves, nor yet allow those who try to go in to do so.
Alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You destroy widow’s houses, even while pretending to make long prayers; therefore you shall receive greater condemnation.
15 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna )
Alas for you, teachers of the law and Pharisees, hypocrites that you are! You scour land and sea to make a single convert, and, when he is gained, you make him twice as deserving of the Pit as you are yourselves. (Geenna )
16 “Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
Alas for you, you blind guides! You say ‘if any answer by the Temple, his oath counts for nothing; but, if any one swears by the gold of the Temple, his oath is binding him’!
17 Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
Fools that you are and blind! Which is the more important? The gold? Or the Temple which has given sacredness to the gold?
18 Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
You say, too, ‘If any one swears by the altar, his oath counts for nothing, but, if any one swears by the offering placed on it, his oath is binding on him’!
19 Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
Blind indeed! Which is the more important? The offering? or the altar which gives sacredness to the offering?
20 Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
Therefore a man, swearing by the altar, swears by it and by all that is on it,
21 Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
and a man, swearing by the Temple, swears by it and by him who dwells in it,
22 Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
while a man, swearing by Heaven, swears by the throne of God, and by him who sits upon it.
23 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
Alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You pay tithes on mint, fennel, and caraway seed, and have neglected the weightier matters of the Law — justice, mercy, and good faith. These last you ought to have put into practice, without neglecting the first.
24 Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
You blind guides, to strain out a gnat and to swallow a camel!
25 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
Alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You clean the outside of the cup and the dish, but inside they are filled with the results of greed and self-indulgence.
26 Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
You blind Pharisee! First clean the inside of the cup and the dish, so that the outside may become clean as well.
27 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
Alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You are like whitewashed tombs, which indeed look fair outside, while inside they are filled with dead men’s bones and all kinds of filth.
28 Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
It is the same with you. Outwardly, and to others, you have the look of religious men, but inwardly you are full of hypocrisy and sin.
29 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
Alas for you, Teachers of the Law and Pharisees, hypocrites that you are! You build the tombs of the Prophets, and decorate the monuments of religious men,
30 Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
and say ‘Had we been living in the days of our ancestors, we should have taken part in their murder of the Prophets!
31 Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
By doing this you are furnishing evidence against yourselves that you are true children of the men who murdered the Prophets.
32 To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
Fill up the measure of your ancestor’s guilt.
33 “Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna )
You serpents and brood of vipers! How can you escape being sentenced to the Pit? (Geenna )
34 Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
That is why I send you Prophets, wise men, and Teachers of the Law, some of whom you will crucify and kill, and some of whom you will scourge in your Synagogues, and persecute from town to town;
35 Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
in order that upon your heads may fall every drop of innocent ‘blood split on earth,’ from the blood of innocent Abel down to that of Zechariah, Barachiah’s son, whom you murdered between the Temple and the altar.
36 Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
All this, I tell you, will come home to the present generation.
37 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
Jerusalem! Jerusalem! She who slays the Prophets and stones the messengers sent to her — Oh, how often have I wished to gather your children round me, as a hen gathers her brood under her wings, and you would not come!
38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
Verily, your house is left to you desolate!
39 Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
For nevermore, I tell you, shall you see me, until you say — ‘Blessed is He who comes in the Name of the Lord!’”