< Mattiyu 23 >
1 Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
Then Jesus spoke to the multitudes, and to his disciples,
2 “Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
saying, The scribes and the Pharisees sit in the seat of Moses.
3 Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
All, therefore, whatever they bid you, do and observe; but do not according to their works; for they say, and do not.
4 Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
They bind heavy burdens, and lay them on men's shoulders, and will not themselves move them with a finger.
5 “Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
And all their works they do to be observed by men. They make broad their phylacteries, and enlarge their fringes,
6 suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
and love the first place at feasts, and the chief seats in the synagogues,
7 suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
and salutations in the markets, and to be called by men, Rabbi.
8 “Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
But be not ye called Rabbi; for one is your teacher; and ye are all brethren.
9 Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
And call no one your father on the earth; for one is your father, he who is in heaven.
10 Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
Nor be ye called leaders; for one is your leader, the Christ.
11 Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
But the greatest among you will be your servant.
12 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
And whoever shall exalt himself will be humbled; and whoever shall humble himself will be exalted.
13 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
But woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites I because ye shut up the kingdom of heaven against men; for ye go not in yourselves, nor suffer those who are entering to go in.
15 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna )
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye compass sea and land to make one proselyte; and when he is made, ye make him two-fold mole a son of hell than yourselves. (Geenna )
16 “Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
Woe to you, blind guides, that say, Whoever sweareth by the temple, it is nothing; but whoever sweareth by the gold of the temple, is bound.
17 Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
Fools and blind I for which is greater, the gold, or the temple that sanctifieth the gold?
18 Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
And, Whoever sweareth by the altar, it is nothing; but whoever sweareth by the gift that is upon it, is bound.
19 Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
Blind men! For which is greater, the gift, or the altar flint sanctifieth the gift?
20 Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
He then who sweareth by the altar, sweareth by it, and by all that is upon it;
21 Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
and he that sweareth by the temple, sweareth by it, and by him who dwelleth in it;
22 Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
and he who sweareth by heaven, sweareth by the throne of God, and by him who sitteth thereon.
23 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye pay tithes of the mint, and the dill, and the cummin, and have omitted the weightier matters of the Law, justice, and mercy, and faith; these ought ye to have done, and not to leave those undone.
24 Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
Blind guides! who strain out a gnat, and swallow a camel.
25 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye make clean the outside of the cup and the platter, but within they are full of robbery and licentiousness.
26 Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
Blind Pharisee! cleanse first the inside of the cup, that its outside side also may become clean.
27 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! for ye are like whited sepulchres, which outwardly indeed appear beautiful, but within are full of dead men's bones, and of all uncleanness.
28 Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
Even so ye also outwardly appear righteous to men, but within ye are full of hypocrisy and iniquity.
29 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
Woe to you, scribes and Pharisees, hypocrites! because ye build the sepulchres of the prophets, and adorn the tombs of the righteous,
30 Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
and say, If we had been in the days of our fathers, we would not have been partakers with them in the blood of the prophets.
31 Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
So that ye bear witness against yourselves, that ye are the sons of those who killed the prophets.
32 To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
Fill ye up then the measure of your fathers!
33 “Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna )
Serpents, brood of vipers! how can ye escape the punishment of hell? (Geenna )
34 Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
Therefore, behold, I send to you prophets, and wise men, and scribes; some of them ye will kill and crucify, and some of them ye will scourge in your synagogues, and persecute from city to city;
35 Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
that on you may come all the righteous blood shed upon the earth, from the blood of righteous Abel to the blood of Zechariah, son of Barachiah, whom ye slew, between the temple and the altar.
36 Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
Truly do I say to you, All these things will come upon this generation.
37 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
Jerusalem, Jerusalem, that killeth the prophets, and stoneth those who are sent to her! How often would I have gathered thy children together, as a hen gathereth her chickens under her wings, and ye would not!
38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
Lo! your house is left to you desolate.
39 Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
For I say to you, Ye will not see me henceforth, till ye shall say, Blessed is he that cometh in the name of the Lord.