< Mattiyu 23 >

1 Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
Then Jesus spoke to the crowds, and to his disciples,
2 “Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
saying: “The scribes and the Pharisees have sat down in the chair of Moses.
3 Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
Therefore, all things whatsoever that they shall say to you, observe and do. Yet truly, do not choose to act according to their works. For they say, but they do not do.
4 Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
For they bind up heavy and unbearable burdens, and they impose them on men’s shoulders. But they are not willing to move them with even a finger of their own.
5 “Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
Truly, they do all their works so that they may be seen by men. For they enlarge their phylacteries and glorify their hems.
6 suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
And they love the first places at feasts, and the first chairs in the synagogues,
7 suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
and greetings in the marketplace, and to be called Master by men.
8 “Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
But you must not be called Master. For One is your Master, and you are all brothers.
9 Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
And do not choose to call anyone on earth your father. For One is your Father, who is in heaven.
10 Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
Neither should you be called teachers. For One is your Teacher, the Christ.
11 Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
Whoever is greater among you shall be your minister.
12 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
But whoever has exalted himself, shall be humbled. And whoever has humbled himself, shall be exalted.
13 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
So then: Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites! For you close the kingdom of heaven before men. For you yourselves do not enter, and those who are entering, you would not permit to enter.
Woe to you scribes and Pharisees, you hypocrites! For you consume the houses of widows, praying long prayers. Because of this, you shall receive the greater judgment.
15 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna g1067)
Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites! For you travel around by sea and by land, in order to make one convert. And when he has been converted, you make him twice the son of Hell that you are yourselves. (Geenna g1067)
16 “Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
Woe to you, blind guides, who say: ‘Whoever will have sworn by the temple, it is nothing. But whoever will have sworn by the gold of the temple is obligated.’
17 Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
You are foolish and blind! For which is greater: the gold, or the temple that sanctifies the gold?
18 Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
And you say: ‘Whoever will have sworn by the altar, it is nothing. But whoever will have sworn by the gift that is on the altar is obligated.’
19 Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
How blind you are! For which is greater: the gift, or the altar that sanctifies the gift?
20 Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
Therefore, whoever swears by the altar, swears by it, and by all that is on it.
21 Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
And whoever will have sworn by the temple, swears by it, and by him who dwells in it.
22 Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
And whoever swears by heaven, swears by the throne of God, and by him who sits upon it.
23 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites! For you collect tithes on mint and dill and cumin, but you have abandoned the weightier things of the law: judgment and mercy and faith. These you ought to have done, while not omitting the others.
24 Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
You blind guides, straining out a gnat, while swallowing a camel!
25 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites! For you clean what is outside the cup and the dish, but on the inside you are full of avarice and impurity.
26 Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
You blind Pharisee! First clean the inside of the cup and the dish, and then what is outside becomes clean.
27 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites! For you are like whitewashed sepulchers, which outwardly appear brilliant to men, yet truly, inside, they are filled with the bones of the dead and with all filth.
28 Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
So also, you certainly appear to men outwardly to be just. But inwardly you are filled with hypocrisy and iniquity.
29 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
Woe to you, scribes and Pharisees, you hypocrites, who build the sepulchers of the prophets and adorn the monuments of the just.
30 Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
And then you say, ‘If we had been there in the days of our fathers, we would not have joined with them in the blood of the prophets.’
31 Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
And so you are witnesses against yourselves, that you are the sons of those who killed the prophets.
32 To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
Complete, then, the measure of your fathers.
33 “Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna g1067)
You serpents, you brood of vipers! How will you escape from the judgment of Hell? (Geenna g1067)
34 Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
For this reason, behold, I send to you prophets and wise men, and scribes. And some of these you will put to death and crucify; and some you will scourge in your synagogues and persecute from city to city,
35 Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
so that upon you may fall all the blood of the just, which has been shed upon the earth, from the blood of Abel the just, even to the blood of Zechariah the son of Barachiah, whom you killed between the temple and the altar.
36 Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
Amen I say to you, all these things shall fall upon this generation.
37 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
Jerusalem, Jerusalem! You kill the prophets and stone those who have been sent to you. How often I have wanted to gather your children together, in the way that a hen gathers her young under her wings. But you were not willing!
38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
Behold, your house shall be abandoned to you, having been deserted.
39 Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
For I say to you, you shall not see me again, until you say: ‘Blessed is he who comes in the name of the Lord.’”

< Mattiyu 23 >