< Mattiyu 21 >

1 Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
U Yesu neamanyisigwa akwa ekapika pakupi ne Yelusalemu hange ekalongola sunga kuBethfage, kulugulu nuka mezeituni, hange u Yesu wihaatuma iamanyisigwa abiili.
2 yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
Wikaaila, longoli kukesale nekakunlongeela, sunga mukumiona ndogwe etungilwe palungwanso, nung'wa ndogwa palung'wi nuyo. Itungueli nukuileta kung'waane.
3 In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
Anga muntu wihi wamuila kehi kua nelanso, mukulunga, 'Mukulu uitakile,' numuntu nuanso ukukaya kumugimbwa mize palung'wi nizo.
4 Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
Ikani nelanso inge ilo naelekeiye kuanyahedagu kusinja ligeelekele. Wikaaila.
5 “Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
Aeli iana akisungu akasayuni, egoza, umutimi wako upembilye kung'waanyu, mupolo hange unaulie mundogwe, nung'wa ndogwe mugoha, ng'wa ndogwe mudabu.
6 Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
Hange iamanyisigwa ekalongola ekituma anga u Yesu naualagiiye.
7 Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
Ikamualeta undogwe nu ng'waa ndogwe, nukueka iang'wenda migulyaao, nu Yesu wikikie nung'wanso.
8 Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
Iidu mumilundo ekaila iangwenda ao munzila niauye ehatema imatambi kupuma mumahota nukaile munzila.
9 Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
Iumbi naelemutongee u Yesu nawa naiamulyatile iha hulya mduli, nukulunga, ''Hosana kung'wana wang'wa Daudi! Ukembelilwe uzile kulima lamukulu; Hosana migulwa kukila.
10 Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
U Yesu paekapika kuYelusalemu, kesale kehi kekitumba nukulunga, ''Uyu nyenyu?
11 Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
Iumbe lekalunga, ''Uyu Yesu munyakidagu, kupuma kunazaleti akuGalilaya.
12 Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
Hange u Yesu wekingela mitekeelo ( ang'wi Tunda. Akaazunsa ehi hunzi naiakugulya nukugula mitekeelo. Wekapeula ga numeza neyaantu nae akukaila impia ne maintu naagulya nkume.
13 Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
Wikaaila, ''Iandekile, ''Ito lane lekutula ito nelakulompela, kuite unyenye mametenda ikulungu laii.
14 Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
Hange iapulu nea kilele ika miziila mitekeelo, nung'wenso wikaakomya.
15 Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
Kuite kumatungo eakulu amakuhani neaandeki naiaine imakula naumiyumi, hange naeigule iang'enya ahuzugalya mitekeelo nukulunga, ''Hosana ng'wana wang'wa Daudi, ''ihaambwa makuo.
16 Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
Ikamuila, ''Wigulene nehe kulambulwa neantu awa? U Yesu wikaaila, ''Ee! kuite muikele kusoma, kupuma mumelomo ang'enya neadabu neakankamukete likimo lupikile.
17 Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
Hange u Yesu wikaaleka nuikulongola kunzi nakisale mu Bethania nukulala kuko.
18 Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
Ikedaudau nausukile mukesali, aeukete nzala.
19 Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn g165)
Wikaleona ikota mumpelompelo anzila. Wikalehanga, kuite shanga wikalya angakentu, mung'wanso inge ematutu du. Akauele, Itule tile inkali kung'waako lukulu hange. ''Hange itungu lelo imtini wekuma (aiōn g165)
20 Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
Amanyisigwa akwe naiaine, ikakulwa nukulunga, yatuleka ule umtini wuma nkua eng'wi?
21 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
U Yesu wikasusha nukulunga, ''Tai kumuila, ang'wi mihutula nuuhueli muleke kuailya, shanga mukituma eke nekitumilwe kumtini udu, kuite mukuuila ate ulugulu, uholwe ugung'we mubahali, yukutula.
22 In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
Kehi nemukulompa kusola, kunu eze muhuie mukusengiilya.
23 Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
U Yesu naupikile mutekeelo, akulu amakuhane anyampala antu ekamuhanga imalungo naukumanyisa nukukolya, kuuhumi ke ukituma imakani aya? Hange nyenyu nukupee uhumi uwu?
24 Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
U Yesu wihasusha nukuaila, nunene hange kumukolya ikolyo nen'wi. Ang'wi mukumbila, nunene uu kumuila kuuhumi ke nekituma imakani aya.
25 Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
Ubadisigwa nuang'wa Yohana aeupumile pee, kulumdane ang'wi kuantu? Ikiholya ienso, akalunga, anga kulunge, aeupumile kilunde ukuuila, nehe mukahita kuhuila?
26 In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
Kuite anga kulunge, aeupumile kuantu, ''kogopile imaumbie, kunsoko ehi aine uYohana kena munyakedagu.''
27 Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
Hange ekasusha kung'wa Yesu nukulunga, ''Shakuine'' Nung'wenso wikaaila gwa, ''Nunene singa kumuila kuushumi he kituma emakani aya.
28 “Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
Kuite mukusinga ntuni? Umuntu nukete iama abiili Wikenda kung'wi nukumuila, Ng'waane, longola witume umulemo mumugunda nuamezabebu.
29 “Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
Lelo, ''Ung'wana wikasusha nukulunga, shaninzuu, kuite panyambele wikakaila imasigo akwe nukulongola.
30 “Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
Nu muntu nuanso wikalongola kung'wana nuanso akasusha nukulunga ninzuu, Mukulu, huite shanga wekenda.
31 “Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
Nuule kuawa neabiili nuilumile anga nuTata wakwe nauloilwe? Ikalunga, ''Ng'wana nuangwandyo'' U Yesu wikaaila, ''Itai kumuila, iamanangwa neakosi ahingela muutemi wang'wi Tunda kuleka hanza unyenye hingela.
32 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
Kundogoilyo u Yohana auzile kitalanyu kunzila nenguloku, kuite singa meka muhuela, mutungo ia manangwa nea kosi akamuhuela. Nu nyenye naimuine nelanso lekole, shanga mekaungana nsoko mieka mumuluile.
33 “Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
Tegeeli ikilingasiilo nekiuya, aukule muntu, umuntu aukele ieneo ikulu nelihi. Auteme imizabibu, unkakitiila, wikazipya nihiseme nekakukamula imagai, akazenga numuhala nualindi nukuliliha kuagaza zabibu. Hange wekenda kehengiza.
34 Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
Imatungu amaogola amizabibu naeuhugee, wikaatuma atuungwa ang'wi, Umuya ekamubulega, nu muya ung'wi ikamukua namagwe.
35 “Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
Kuite awe neelima izabibu ikazihola eihimi akwe, ihamuhua ung'wi, Umuiye eka mubalaga, nu muya ung'wi ikamukua namagwe.
36 Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
Kumkua nengiza, umugole wikaatuma atungwi angiza, eeelu kukila awa neangwandyo, huite awa neelima akaaleda hange wudu.
37 A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
Nai akahila nanso umuhulu nuanso akamutuma latalao uug'waalawe nukulunga, ahumukulyaumngwane.
38 “Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
Kuite awa neelma emezabibu naeamwine umuhumba nuanso, Akiela, Uyu musali, Nzii, kumbulage nukuhola uusali.
39 Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
Uu ekamuhola, ekamugume kunzi na mugunda nua mizabibu nukumubulaga.
40 “To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
Itee umukola mugunda nua mizabibu nuzile, utenda uli ialemi amezabibu?
41 Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
Ikamuila, ''Ukuabipya iantu nuanso abi kunzila aulaki kukila, ne hange ukusalisha umugunda nua mizabibu kulumiangeza, iantu neahuli pa kunzila amezabibu neakahonda''.
42 Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
U Yesu wikaaila '' Shamusomilene numaandeko,' Igwe nealatulile iaashi naina igwa ikulu nelaukundeki, Ile lepumile kumukulu, hange ukuleta ikuilwa kumiho iluu?
43 “Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
Uu kumuila, Utemi wang'wi Tunda ukuholwa kupuma kitalanyu nukupegwa ihe nekee inkali yalawe.
44 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
Wehi nuekagwa nugwe nelanso ukubungwa ninoo. Kuite kuehi nelelumugwila, lekumusia.
45 Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
Ikulu amakuhani nea mafalisayo naeakija ilingasilyo yakwe, ikaona kena akulambulwa enso.
46 Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.
Kuite kela naealoilwe kugoola mikono migulya lakwe, akagopa umilundo, kunsoko iantu aeamugozile anga munyakidagu.

< Mattiyu 21 >