< Mattiyu 21 >
1 Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
Když se blížili k Jeruzalému a přišli do Betfage u Olivové hory, poslal Ježíš dva ze svých učedníků napřed
2 yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
a řekl jim: „Jakmile přijdete do vesnice tady před námi, najdete přivázanou oslici s oslátkem. Odvažte je a přiveďte mi je.
3 In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
Kdyby se vás někdo ptal, co děláte, řekněte, co předpověděl prorok:
4 Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
5 “Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
‚Oznamte Jeruzalému: Tvůj král přichází k tobě, tichý, přijíždí na oslátku.‘“
6 Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
Učedníci šli a udělali vše podle Ježíšova příkazu.
7 Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
Přivedli oslici i oslátko, místo sedla podložili své pláště a na ně posadili Ježíše.
8 Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
Mnozí z davu pokládali své pláště na cestu, jiní osekávali větve ze stromů a zdobili jimi cestu.
9 Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
Průvod lidí, který ho obklopoval zepředu i zezadu, volal:
10 Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
Když vjel do Jeruzaléma, celé město vřelo a lidé se vzrušeně ptali: „Kdo je to?“
11 Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
Z průvodu se ozývalo: „To je Ježíš, ten prorok z galilejského Nazaretu!“
12 Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
Ježíš pak vešel do chrámu a vyhnal všechny, kteří tu prodávali a kupovali, zpřevracel stoly směnárníků a prodavačů obětních holubů
13 Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
a řekl jim: „Písmo praví: Boží chrám je místem pro modlitbu, ale vy jste z něj udělali zlodějské doupě!“
14 Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
Na chrámovém nádvoří se kolem něj shlukli slepí a chromí a on je uzdravoval.
15 Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
Když však velekněží a vykladači zákona viděli ty zázraky a slyšeli, jak i malé děti volají v chrámu: „Sláva Davidovu synu!“velmi je to pobouřilo.
16 Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
Vyčítali mu: „Neslyšíš, co volají?“On jim odpověděl: „Ovšem. Což jste nečetli v Písmu: I křik nemluvňat chválí Boha.“
17 Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
Nechal je být a odešel zpět do Betanie, kde zůstal přes noc.
18 Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
Když se ráno vracel do Jeruzaléma, dostal hlad.
19 Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn )
Všiml si fíkovníku u cesty. Když však přišel ke stromu, viděl, že na něm nejsou žádné plody, ale jen listí. Řekl: „Už nikdy se na tobě neurodí ovoce!“A ten fíkovník rázem uschl. (aiōn )
20 Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
Když to viděli učedníci, udiveně říkali: „Jak jsi to dokázal, že ten fíkovník tak rychle uschl?“
21 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
Ježíš jim odpověděl: „Skutečně vám říkám, věříte-li bez pochybností, můžete dělat i větší věci než to, co jste nyní viděli. Kdybyste rozkázali této hoře, aby se pohnula a sesula do moře, pak se to stane.
22 In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
Všechno je pro vás dosažitelné, zač se s vírou modlíte.“
23 Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
Když pak zas učil v chrámu, přišli k němu velekněží a židovští předáci a ptali se ho: „Jakým právem zde takto jednáš? Kdo ti k tomu dal moc?“
24 Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
„Řeknu vám to, ale nejprve odpovězte vy na moji otázku: Křtil Jan z pověření Boha nebo lidí?“Říkali si mezi sebou: „Odpovíme-li, že byl od Boha, namítne nám, proč jsme tedy nevěřili jeho slovům. A jestliže odpovíme záporně, pak abychom se báli davu, protože Jana všichni považují za proroka.“
25 Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
26 In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
27 Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
Tak nakonec odpověděli: „Nevíme.“Nato Ježíš: „Ani já vám tedy neřeknu, kdo stojí za mnou.
28 “Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
Jak byste rozsoudili takový případ? Jeden muž měl dva syny a řekl jednomu z nich: ‚Jdi dnes pracovat na vinici!‘
29 “Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
On však odpověděl: ‚Nechce se mi!‘Potom si to ale rozmyslel a šel.
30 “Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
O totéž požádal druhého syna. Ten řekl: ‚Ano, půjdu, ‘ale nešel.
31 “Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
Který z těch dvou synů poslechl svého otce?“Oni odpověděli: „Ten první.“„Právě tak, “řekl Ježíš, „vás podvodníci a prostitutky předbíhají do Božího království.
32 Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
Jan Křtitel vám ukázal správnou cestu k pokání; vy jste na něj nedali, ale tihle lidé ano. Ani to vás nezahanbilo a stejně jste neposlechli.
33 “Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
Nyní si poslechněte jiný příběh: Byl jeden hospodář, který založil vinici. Obehnal ji plotem, zřídil v ní lis a postavil věž pro hlídače. Pak vinici pronajal vinařům a odcestoval.
34 Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
V době vinobraní poslal k vinařům své zástupce, aby vybrali jeho podíl.
35 “Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
Vinaři je však popadli, jednoho zbili, druhého utloukli a dalšího ukamenovali. Hospodář tedy poslal další muže; tentokrát jich bylo více. Ale vinaři s nimi naložili stejně.
36 Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
37 A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
Nakonec k nim tedy poslal svého syna. Myslel si, že alespoň před ním budou mít respekt.
38 “Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
Ale když jej viděli přicházet, řekli si: ‚To je dědic! Zabijme ho a vinice bude naše!‘
39 Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
Popadli ho, vyvlekli z vinice ven a zabili.
40 “To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
Co myslíte, že udělá hospodář s těmi vinaři, až se vrátí?“
41 Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
Odpověděli mu: „Ty zločince dá bez milosti popravit a vinici pronajme lidem, kteří mu budou svědomitě odvádět výnosy.“
42 Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
Potom se jich Ježíš zeptal, zda znají slova Písma: „Kámen, který stavitelé neustále odkládali, sloužil nakonec jako hlavní svorník klenby. Jaký to div! Jak zvláštní věc Bůh udělal!“
43 “Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
„Chci tím říci, že vám Bůh odejme správu nad svým královstvím a svěří ji lidem, kteří mu budou odvádět, co mu patří.
44 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
Kdo ten kámen nedá na pravé místo, zakopne o něj, nebo ho kámen rozdrtí.“
45 Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
Když velekněží a farizejové slyšeli tyto příměry, pochopili, že mluví o nich.
46 Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.
Chtěli ho zatknout, ale báli se davu, protože všichni považovali Ježíše za proroka.