< Mattiyu 20 >
1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
For himlenes rike er likt en husbond som gikk ut tidlig om morgenen for å leie arbeidere til sin vingård.
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
Og da han var blitt enig med arbeiderne om en penning om dagen, sendte han dem bort til sin vingård.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
Og han gikk ut ved den tredje time og så andre stå ledige på torvet,
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
og til dem sa han: Gå også I bort til vingården, og hvad rett er, vil jeg gi eder. Og de gikk avsted.
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
Atter gikk han ut ved den sjette og den niende time og gjorde likeså.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
Og han gikk ut ved den ellevte time og fant andre stående der, og han sa til dem: Hvorfor står I her ledige hele dagen?
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
De sa til ham: Fordi ingen har leid oss. Han sa til dem: Gå også I bort til vingården!
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
Men da det var blitt aften, sa vingårdens herre til sin forvalter: Kall arbeiderne frem og gi dem deres lønn; begynn med de siste og end med de første!
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
Så kom de som var leid ved den ellevte time, og de fikk hver sin penning.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
Men da de første kom, tenkte de at de skulde få mere; men de fikk hver sin penning de også.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
Men da de fikk den, knurret de mot husbonden og sa:
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
Disse siste har bare vært her en time, og du har gjort dem like med oss som har båret dagens byrde og hete.
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
Men han svarte en av dem og sa: Min venn! jeg gjør dig ikke urett, blev du ikke enig med mig om en penning?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Ta ditt og gå! Men jeg vil gi denne siste like så meget som dig.
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Eller har jeg ikke lov til å gjøre med mitt hvad jeg vil? eller er ditt øie ondt fordi jeg er god?
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
Således skal de siste bli de første, og de første de siste; for mange er kalt, men få utvalgt.
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
Og da Jesus drog op til Jerusalem, tok han de tolv disipler til side og sa til dem på veien:
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
Se, vi går op til Jerusalem, og Menneskesønnen skal overgis til yppersteprestene og de skriftlærde, og de skal dømme ham til døden
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
og overgi ham til hedningene til å spottes og hudstrykes og korsfestes; og på den tredje dag skal han opstå.
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Da gikk Sebedeus-sønnenes mor til ham med sine sønner, falt ned for ham og bad ham om noget.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
Han sa til henne: Hvad vil du? Hun sa til ham: Si at disse mine to sønner skal sitte, den ene ved din høire og den andre ved din venstre side i ditt rike!
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
Men Jesus svarte og sa: I vet ikke hvad det er I ber om. Kan I drikke den kalk jeg skal drikke? De sa til ham: Det kan vi.
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
Han sa til dem: Min kalk skal I nok drikke; men å sitte ved min høire og ved min venstre side, det tilkommer det ikke mig å gi nogen, men det gis dem som det er beredt av min Fader.
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
Da de ti hørte dette, blev de harme på de to brødre.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
Men Jesus kalte dem til sig og sa: I vet at fyrstene hersker over sine folk, og deres stormenn bruker makt over dem.
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
Så skal det ikke være blandt eder; men den som vil bli stor iblandt eder, han skal være eders tjener,
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
og den som vil være den første blandt eder, han skal være eders træl,
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
likesom Menneskesønnen ikke er kommet for å la sig tjene, men for selv å tjene og gi sitt liv til en løsepenge for mange.
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
Og da de gikk ut fra Jeriko, fulgte meget folk ham.
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
Og se, to blinde satt ved veien, og da de hørte at det var Jesus som gikk forbi, ropte de: Miskunn dig over oss, Herre, du Davids sønn!
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
Folket truet dem at de skulde tie; men de ropte enda mere og sa: Herre, miskunn dig over oss, du Davids sønn!
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
Og Jesus stod stille og kalte på dem og sa: Hvad vil I jeg skal gjøre for eder?
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
De sa: Herre! at våre øine må bli oplatt!
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
Da ynkedes Jesus inderlig og rørte ved deres øine; og straks fikk de sitt syn igjen, og de fulgte ham.