< Mattiyu 20 >
1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
For the kingdom of heaven is like a man that is an householder, who went out early in the morning to hire labourers into his vineyard.
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
And when he had agreed with the labourers for a penny a day, he sent them into his vineyard.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
And he went out about the third hour, and saw others standing idle in the marketplace,
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
And said to them; Go ye also into the vineyard, and whatever is right I will give you. And they went.
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
Again he went out about the sixth and ninth hour, and did the same.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
And about the eleventh hour he went out, and found others standing idle, and saith to them, Why stand ye here all the day idle?
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
They say to him, Because no man hath hired us. He saith to them, Go ye also into the vineyard; and whatever is right, that shall ye receive.
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
So when evening was come, the lord of the vineyard saith to his steward, Call the labourers, and give them their hire, beginning from the last to the first.
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
And when they came that were hired about the eleventh hour, they received every man a penny.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
But when the first came, they supposed that they should receive more; and they likewise received every man a penny.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
And when they had received it, they murmured against the master of the house,
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
Saying, These last have worked but one hour, and thou hast made them equal to us, who have borne the burden and heat of the day.
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
But he answered one of them, and said, Friend, I do thee no wrong: didst thou not agree with me for a penny?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Take that which is thine, and go thy way: I will give to this last, even as to thee.
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Is it not lawful for me to do what I will with my own? Is thy eye evil, because I am good?
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
So the last shall be first, and the first last: for many are called, but few chosen.
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
And Jesus going up to Jerusalem took the twelve disciples aside in the way, and said to them,
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
Behold, we go up to Jerusalem; and the Son of man shall be betrayed to the chief priests and to the scribes, and they shall condemn him to death,
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
And shall deliver him to the Gentiles to mock, and to scourge, and to crucify him: and the third day he shall rise again.
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Then came to him the mother of Zebedee’s children with her sons, worshipping him, and desiring a certain thing of him.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
And he said to her, What wilt thou? She saith to him, Grant that these my two sons may sit, the one on thy right hand, and the other on the left, in thy kingdom.
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
But Jesus answered and said, Ye know not what ye ask. Are ye able to drink of the cup that I shall drink of, and to be baptized with the baptism that I am baptized with? They say to him, We are able.
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
And he saith to them, Ye shall drink indeed of my cup, and be baptized with the baptism that I am baptized with: but to sit on my right hand, and on my left, is not mine to give, but it shall be given to them for whom it is prepared by my Father.
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
And when the ten heard it, they were moved with indignation against the two brethren.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
But Jesus called them to him, and said, Ye know that the princes of the Gentiles exercise dominion over them, and they that are great exercise authority upon them.
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
But it shall not be so among you: but whoever will be great among you, let him be your minister;
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
And whoever will be chief among you, let him be your servant:
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Even as the Son of man came not to be ministered to, but to minister, and to give his life a ransom for many.
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
And as they departed from Jericho, a great multitude followed him.
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
And, behold, two blind men sitting by the way side, when they heard that Jesus passed by, cried out, saying, Have mercy on us, O Lord, thou Son of David.
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
And the multitude rebuked them, that they should hold their peace: but they cried the more, saying, Have mercy on us, O Lord, thou Son of David.
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
And Jesus stood still, and called them, and said, What will ye that I shall do to you?
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
They say to him, Lord, that our eyes may be opened.
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
So Jesus had compassion on them, and touched their eyes: and immediately their eyes received sight, and they followed him.