< Mattiyu 20 >
1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
For the kingdom of the heavens, is like, a man, a householder, —who went forth with the morning, to hire labourers into his vineyard;
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
and, when he had agreed with the labourers for a denary the day, he sent them into his vineyard.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
And, going forth about the third hour, he saw others, standing in the market-place, unemployed;
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
and, to them, he said—ye also, go your way into the vineyard, and, whatsoever may be right, I will give you;
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
and, they, departed. And, again, going forth about the sixth and ninth hour, he did likewise.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
And, about the eleventh, going forth, he found others, standing, and saith unto them—Why, here, stand ye, all the day, unemployed?
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
They say unto him—Because, no one, hath hired, us. He saith unto them—Ye also, go your way into the vineyard.
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
And, when evening came, the master of the vineyard saith unto his steward—Call the labourers, and pay the hire, —beginning from the last, unto the first.
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
And they of the eleventh hour, coming, received severally a denary.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
And, when the first came, they supposed that, more, they should receive, —and, they also, received severally a denary.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
And, having received it, they began to murmur against the householder, saying—
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
These last, one hour, wrought, and thou hast made them, equal unto us, who have borne the burden of the day, and the scorching heat.
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
And, he, answering, unto one of them, said, —Friend! I wrong thee not: Was it not, for a denary, thou didst agree with me?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Take thine own, and go thy way; but I please, unto this last, to give, as also to thee:
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Is it not allowed me to do, what I please, with my own? or is, thine eye, evil, because I good?
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
Thus, shall be—The last first, and the first last.
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
And, Jesus, being about to go up unto Jerusalem, took unto him the twelve [disciples], apart, and, in the way, he said unto them—
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
Lo! we are going up unto Jerusalem; and, the Son of Man, will be delivered up unto the chief-priests and Scribes, and they will condemn him, [to death],
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
And deliver him up unto the nations, to mock and to scourge and to crucify, —and, on the third day, he will, arise.
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Then came unto him the mother of the sons of Zebedee, with her sons, bowing down, and asking something from him.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
And, he, said to her—What desirest thou? She saith unto him—Bid, that these my two sons may sit, one on thy right hand, and one on thy left, in thy kingdom.
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
But Jesus, answering, said—Ye know not what ye are asking: Are ye able to drink the cup, which, I, am about to drink; They say unto him—We are able.
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
He saith unto them—My cup, indeed, ye shall drink; but, to sit on my right hand and on my left, is not mine to give, —except unto those for whom it hath been prepared by my Father.
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
And the ten, hearing, were sorely displeased, concerning the two brethren.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
But, Jesus, calling them near, said—Ye know that, the rulers of the nations, lord it over them, and, the great ones, wield authority over them:
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
Not so, is it, among you, —but, whosoever shall desire, among you, to become, great, shall be, your minister;
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
And, whosoever shall desire, among you, to be first, shall be, your servant: —
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Just as, the Son of Man, came not to be ministered unto, but to minister, and to give his life a ransom instead of many.
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
And, as they were going forth from Jericho, there followed him a great multitude;
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
and lo! two blind men, sitting beside the road, hearing that Jesus was passing by, cried aloud saying—Lord! have mercy on us! Son of David!
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
But the multitude rebuked them, that they might hold their peace. But, they, the more, cried aloud, saying—Lord, have mercy on us! Son of David!
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
And, standing still, Jesus called them, and said—What desire ye I should do for you?
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
They say unto him—Lord! that, our eyes, may open.
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
And, moved with compassion, Jesus touched their eyes, —and, straightway, they recovered sight, and followed him.