< Mattiyu 20 >
1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
For the kingdome of heauen is like vnto a certaine, housholder, which went out at the dawning of the day to hire labourers into his vineyarde.
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
And he agreed with the labourers for a peny a day, and sent them into his vineyard.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
And he went out about the third houre, and sawe other standing idle in the market place,
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
And sayd vnto them, Goe ye also into my vineyard, and whatsoeuer is right, I will giue you: and they went their way.
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
Againe he went out about the sixt and ninth houre, and did likewise.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
And he went about the eleuenth houre, and found other standing idle, and sayd vnto them, Why stand ye here all the day idle?
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
They sayd vnto him, Because no man hath hired vs. He sayd to them, Goe ye also into my vineyard, and whatsoeuer is right, that shall ye receiue.
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
And when euen was come, the master of the vineyard sayd vnto his steward, Call the labourers, and giue them their hire, beginning at the last, till thou come to the first.
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
And they which were hired about ye eleuenth houre, came and receiued euery man a penie.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
Nowe when the first came, they supposed that they should receiue more, but they likewise receiued euery man a penie.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
And when they had receiued it, they murmured against the master of the house,
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
Saying, These last haue wrought but one houre, and thou hast made them equall vnto vs, which haue borne the burden and heate of the day.
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
And hee answered one of them, saying, Friend, I doe thee no wrong: didst thou not agree with me for a penie?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Take that which is thine owne, and go thy way: I will giue vnto this last, as much as to thee.
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Is it not lawfull for me to do as I will with mine owne? Is thine eye euil, because I am good?
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
So the last shalbe first, and the first last: for many are called, but fewe chosen.
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
And Iesus went vp to Hierusalem, and tooke the twelue disciples apart in the way, and said vnto them,
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
Beholde, wee goe vp to Hierusalem, and the Sonne of man shall bee deliuered vnto the chiefe priestes, and vnto the Scribes, and they shall condemne him to death,
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
And shall deliuer him to the Gentiles, to mocke, and to scourge, and to crucifie him, but the third day he shall rise againe.
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Then came to him the mother of Zebedeus children with her sonnes, worshipping him, and desiring a certaine thing of him.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
And he said vnto her, What wouldest thou? She said to him, Graunt that these my two sonnes may sit, the one at thy right hand, and the other at thy left hand in thy kingdome.
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
And Iesus answered and said, Ye know not what ye aske. Are ye able to drinke of the cup that I shall drinke of, and to be baptized with the baptisme that I shalbe baptized with? They said to him, We are able.
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
And he said vnto them, Ye shall drinke in deede of my cup, and shall be baptized with the baptisme, that I am baptized with, but to sit at my right hande, and at my left hand, is not mine to giue: but it shalbe giuen to them for whome it is prepared of my Father.
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
And when the other ten heard this, they disdained at the two brethren.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
Therefore Iesus called them vnto him, and saide, We knowe that the lordes of the Gentiles haue domination ouer them, and they that are great, exercise authoritie ouer them.
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
But it shall not be so among you: but whosoeuer will be great among you, let him be your seruant.
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
And whosoeuer will be chiefe among you, let him be your seruant.
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Euen as the Sonne of man came not to be serued, but to serue, and to giue his life for the ransome of many.
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
And as they departed from Iericho, a great multitude followed him.
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
And beholde, two blinde men, sitting by the way side, when they heard that Iesus passed by, cryed, saying, O Lord, the Sonne of Dauid, haue mercie on vs.
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
And the multitude rebuked them, because they should holde their peace: but they cried the more, saying, O Lord, the Sonne of Dauid, haue mercie on vs.
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
Then Iesus stoode still, and called them, and said, What will ye that I should do to you?
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
They saide to him, Lord, that our eyes may be opened.
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
And Iesus mooued with compassion, touched their eyes, and immediatly their eyes receiued sight, and they followed him.