< Mattiyu 20 >
1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
For the kingdom of heaven is like a landowner who went out early in the morning to hire workers for his vineyard.
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
He agreed to pay the workers one denarius for the day, and sent them to work in his vineyard.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
Around 9 a.m. he went out and saw others without work standing in the marketplace.
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
‘Go and work in the vineyard too, and I'll pay you what's right,’ he told them. So they went to work.
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
Around noon and 3 p.m. he went out and did the same thing.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
At 5 p.m. he went out and found others standing there. ‘Why are you standing around all day doing nothing?’ he asked them.
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
‘Because nobody has hired us,’ they replied. ‘Go and work in the vineyard too,’ he told them.
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
When evening came, the owner of the vineyard told his manager, ‘Call the workers in, and pay them their wages. Begin with the workers hired last and then move on to those hired first.’
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
When those who were hired at 5 p.m. came in, they each received one denarius.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
So when those who were hired first came in, they thought they would get more, but they also received one denarius.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
When they received their pay, they complained to the owner.
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
‘Those who were hired last only worked for an hour, and you've paid them the same as us who worked the whole day in the burning heat,’ they grumbled.
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
The owner answered one of them, ‘My friend, I haven't treated you unfairly. Didn't you agree with me to work for one denarius?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Take your pay and go. I want to pay those who were hired last the same as I paid you.
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Can't I choose to do what I want with my own money? Why should you give me evil looks because I want to do good?’
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
In this way the last shall be first and the first shall be last.”
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
On the way to Jerusalem, Jesus took the twelve disciples aside as they walked along and told them,
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
“Look, we're going to Jerusalem, and the Son of man will be betrayed to the chief priests and religious teachers. They will condemn him to death
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
and hand him over to the foreigners to mock him, whip him, and crucify him. But on the third day he will be raised from the dead.”
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Then the mother of the sons of Zebedee came with her two sons to Jesus. She kneeled down before him to make a request.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
“What is it you are asking me for?” Jesus said to her. “Please appoint my sons to sit beside you in your kingdom, one on your right and the other on your left,” she asked.
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
“You don't know what you're asking,” Jesus told them. “Are you able to drink the cup I'm about to drink?” “Yes, we are able to do that,” they told him.
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
“You will certainly drink from my cup,” he said to them, “but the privilege to sit on my right or on my left isn't mine to give. My Father is the one who has decided who that will be.”
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
When the other ten disciples heard what they had asked, they were annoyed with the two brothers.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
Jesus called them together and told them, “You know that foreign rulers lord it over their subjects, and powerful leaders oppress them.
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
It shall not be like that for you. Whoever among you wants to be the most important will be your servant.
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
Whoever among you wants to be first will be like a slave.
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
In the same way the Son of man didn't come to be served, but to serve, and to give his life as a ransom for many.”
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
As they left Jericho, a huge crowd followed Jesus.
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
Two blind men were sitting at the side of the road. When they heard that Jesus was passing by, they called out, “Have mercy on us, Lord, son of David!”
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
The crowd told them to be quiet, but they shouted even louder, “Have mercy on us, Lord, son of David!”
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
Jesus stopped. He called them over, asking, “What do you want me to do for you?”
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
“Lord, please make us able to see,” they replied.
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
Jesus had pity on them and touched their eyes. Immediately they could see, and they followed him.