< Mattiyu 2 >

1 Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
Ko se je pa Jezus v Betlehemu Judejskem rodil, v dnéh Heroda kralja, glej, pridejo od vzhoda modrijani v Jeruzalem,
2 suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
Govoreč: Kje je kralj Judovski, ki se je rodil? Kajti videli smo zvezdo njegovo na vzhodu, pa smo prišli, da mu se poklonimo.
3 Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
Slišavši pa to kralj Herod, prestraši se, in ves Jeruzalem ž njim.
4 Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
In zbravši vse vélike duhovne in ljudske pismarje, povpraševal jih je, kje se ima Kristus roditi.
5 Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
Oni mu pa rekó: V Betlehemu Judejskem; kajti tako je napisal prerok:
6 “‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
"In ti, Betlehem, zemlja Judova, nikakor nisi najmanji med knezi Judovimi; kajti iz tebe bo izšel vojvoda, kteri bo pasel narod moj Izraelski."
7 Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
Tedaj pokliče Herod skrivaj modrijane, in pozvé od njih na tanko, kedaj se je zvezda prikazala.
8 Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
In poslavši jih v Betlehem, reče: Pojdite in na tanko izprašajte za dete; a ko ga najdete, sporočite mi, da tudi jaz pridem in mu se poklonim.
9 Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
Oni pa, zaslišavši kralja, odidejo. In glej, zvezda, ktero so bili videli na vzhodu, šla je pred njimi, dokler ni prišla in se ustavila nad mestom, kjer je bilo dete.
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
Ko pa ugledajo zvezdo, razveselé se z zeló velikim veseljem.
11 Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
In pridejo v hišo, in najdejo dete z Marijo materjo njegovo; in padejo, ter mu se poklonijo; in odpró zaklade svoje, ter mu prinesó darove: zlato in kadilo in miro.
12 Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
In opomenjeni v spanji, naj se ne vračajo k Herodu, odidejo po drugej poti v svoj kraj.
13 Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
Ko so pa oni odpotovali, glej, prikaže se angelj Gospodov Jožefu v spanji, govoreč: Vstani in vzemi dete in mater njegovo, pa beži v Egipet, in bodi tam, dokler ti ne povem; kajti Herod bo iskal deteta, da bi ga pogubil.
14 Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
On pa vstane in vzeme dete in mater njegovo po noči, in odide v Egipet.
15 inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
In bil je tam do Herodove smrti; da se izpolni, kar je rekel Gospod po preroku, kteri pravi: "Iz Egipta sem poklical sina svojega."
16 Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
Tedaj se Herod, videvši, da so ga modrijani prekanili, zeló raztogotí, ter pošlje in pomori po Betlehemu in po vseh predelih njegovih vse otročiče po dve leti in niže, po času, ki ga je na tanko pozvedel od modrijanov.
17 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
Tedaj se je izpolnilo, kar je rekel prerok Jeremija, govoreč:
18 “An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
"Glas se je slišal v Rami, mnogo jokú in veka in krika; Rahel je plakala za svojimi otroci, in ni se hotela utolažiti, ker jih ni."
19 Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
Ko je pa Herod umrl, glej, prikaže se v spanji angelj Gospodov Jožefu v Egiptu,
20 ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
Govoreč: Vstani in vzemi dete in mater njegovo, in pojdi v zemljo Izraelsko; kajti pomrli so, kteri so iskali detetove duše.
21 Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
On pa vstane in vzeme dete in mater njegovo, in pride v zemljo Izraelsko.
22 Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
Slišavši pa, da kraljuje v Judeji Arhelaj mesto Heroda očeta svojega, zbojí se tje iti; opomenjen pa v spanji, odide v predele Galilejske.
23 ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”
In prišedši tje, nastani se v mestu, ktero se imenuje Nazaret; da se izpolni, kar je rečeno po prerokih: "Nazarečan se bo imenoval."

< Mattiyu 2 >