< Mattiyu 2 >
1 Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
ཨནནྟརཾ ཧེརོད྄ སཾཛྙཀེ རཱཛྙི རཱཛྱཾ ཤཱསཏི ཡིཧཱུདཱིཡདེཤསྱ བཻཏླེཧམི ནགརེ ཡཱིཤཽ ཛཱཏཝཏི ཙ, ཀཏིཔཡཱ ཛྱོཏིཪྻྭུདཿ པཱུཪྻྭསྱཱ དིཤོ ཡིརཱུཤཱལམྣགརཾ སམེཏྱ ཀཐཡམཱསུཿ,
2 suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
ཡོ ཡིཧཱུདཱིཡཱནཱཾ རཱཛཱ ཛཱཏཝཱན྄, ས ཀུཏྲཱསྟེ? ཝཡཾ པཱུཪྻྭསྱཱཾ དིཤི ཏིཥྛནྟསྟདཱིཡཱཾ ཏཱརཀཱམ྄ ཨཔཤྱཱམ ཏསྨཱཏ྄ ཏཾ པྲཎནྟུམ྄ ཨགམཱམ།
3 Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
ཏདཱ ཧེརོད྄ རཱཛཱ ཀཐཱམེཏཱཾ ནིཤམྱ ཡིརཱུཤཱལམྣགརསྠིཏཻཿ སཪྻྭམཱནཝཻཿ སཱརྡྡྷམ྄ ཨུདྭིཛྱ
4 Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
སཪྻྭཱན྄ པྲདྷཱནཡཱཛཀཱན྄ ཨདྷྱཱཔཀཱཾཤྩ སམཱཧཱུཡཱནཱིཡ པཔྲཙྪ, ཁྲཱིཥྚཿ ཀུཏྲ ཛནིཥྱཏེ?
5 Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
ཏདཱ ཏེ ཀཐཡཱམཱསུཿ, ཡིཧཱུདཱིཡདེཤསྱ བཻཏླེཧམི ནགརེ, ཡཏོ བྷཝིཥྱདྭཱདིནཱ ཨིཏྠཾ ལིཁིཏམཱསྟེ,
6 “‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
སཪྻྭཱབྷྱོ རཱཛདྷཱནཱིབྷྱོ ཡིཧཱུདཱིཡསྱ ནཱིཝྲྀཏཿ། ཧེ ཡཱིཧཱུདཱིཡདེཤསྱེ བཻཏླེཧམ྄ ཏྭཾ ན ཙཱཝརཱ། ཨིསྲཱཡེལཱིཡལོཀཱན྄ མེ ཡཏོ ཡཿ པཱལཡིཥྱཏི། ཏཱདྲྀགེཀོ མཧཱརཱཛསྟྭནྨདྷྱ ཨུདྦྷཝིཥྱཏཱི༎
7 Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
ཏདཱནཱིཾ ཧེརོད྄ རཱཛཱ ཏཱན྄ ཛྱོཏིཪྻྭིདོ གོཔནམ྄ ཨཱཧཱུཡ སཱ ཏཱརཀཱ ཀདཱ དྲྀཥྚཱབྷཝཏ྄, ཏད྄ ཝིནིཤྩཡཱམཱས།
8 Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
ཨཔརཾ ཏཱན྄ བཻཏླེཧམཾ པྲཧཱིཏྱ གདིཏཝཱན྄, ཡཱུཡཾ ཡཱཏ, ཡཏྣཱཏ྄ ཏཾ ཤིཤུམ྄ ཨནྭིཥྱ ཏདུདྡེཤེ པྲཱཔྟེ མཧྱཾ ཝཱརྟྟཱཾ དཱསྱཐ, ཏཏོ མཡཱཔི གཏྭཱ ས པྲཎཾསྱཏེ།
9 Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
ཏདཱནཱིཾ རཱཛྙ ཨེཏཱདྲྀཤཱིམ྄ ཨཱཛྙཱཾ པྲཱཔྱ ཏེ པྲཏསྠིརེ, ཏཏཿ པཱུཪྻྭརྶྱཱཾ དིཤི སྠིཏཻསྟཻ ཪྻཱ ཏཱརཀཱ དྲྀཥྚཱ སཱ ཏཱརཀཱ ཏེཥཱམགྲེ གཏྭཱ ཡཏྲ སྠཱནེ ཤིཤཱུརཱསྟེ, ཏསྱ སྠཱནསྱོཔརི སྠགིཏཱ ཏསྱཽ།
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
ཏད྄ དྲྀཥྚྭཱ ཏེ མཧཱནནྡིཏཱ བབྷཱུཝུཿ,
11 Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
ཏཏོ གེཧམདྷྱ པྲཝིཤྱ ཏསྱ མཱཏྲཱ མརིཡམཱ སཱདྡྷཾ ཏཾ ཤིཤུཾ ནིརཱིཀྵཡ དཎྜཝད྄ བྷཱུཏྭཱ པྲཎེམུཿ, ཨཔརཾ སྭེཥཱཾ གྷནསམྤཏྟིཾ མོཙཡིཏྭཱ སུཝརྞཾ ཀུནྡུརུཾ གནྡྷརམཉྩ ཏསྨཻ དརྴནཱིཡཾ དཏྟཝནྟཿ།
12 Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
པཤྩཱད྄ ཧེརོད྄ རཱཛསྱ སམཱིཔཾ པུནརཔི གནྟུཾ སྭཔྣ ཨཱིཤྭརེཎ ནིཥིདྡྷཱཿ སནྟོ ྅ནྱེན པཐཱ ཏེ ནིཛདེཤཾ པྲཏི པྲཏསྠིརེ།
13 Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
ཨནནྟརཾ ཏེཥུ གཏཝཏྨུ པརམེཤྭརསྱ དཱུཏོ ཡཱུཥཕེ སྭཔྣེ དརྴནཾ དཏྭཱ ཛགཱད, ཏྭམ྄ ཨུཏྠཱཡ ཤིཤུཾ ཏནྨཱཏརཉྩ གྲྀཧཱིཏྭཱ མིསརྡེཤཾ པལཱཡསྭ, ཨཔརཾ ཡཱཝདཧཾ ཏུབྷྱཾ ཝཱརྟྟཱཾ ན ཀཐཡིཥྱཱམི, ཏཱཝཏ྄ ཏཏྲཻཝ ནིཝས, ཡཏོ རཱཛཱ ཧེརོད྄ ཤིཤུཾ ནཱཤཡིཏུཾ མྲྀགཡིཥྱཏེ།
14 Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
ཏདཱནཱིཾ ཡཱུཥཕ྄ ཨུཏྠཱཡ རཛནྱཱཾ ཤིཤུཾ ཏནྨཱཏརཉྩ གྲྀཧཱིཏྭཱ མིསརྡེཤཾ པྲཏི པྲཏསྠེ,
15 inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
གཏྭཱ ཙ ཧེརོདོ ནྲྀཔཏེ རྨརཎཔཪྻྱནྟཾ ཏཏྲ དེཤེ ནྱུཝཱས, ཏེན མིསརྡེཤཱདཧཾ པུཏྲཾ སྭཀཱིཡཾ སམུཔཱཧཱུཡམ྄། ཡདེཏདྭཙནམ྄ ཨཱིཤྭརེཎ བྷཝིཥྱདྭཱདིནཱ ཀཐིཏཾ ཏཏ྄ སཕལམབྷཱུཏ྄།
16 Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
ཨནནྟརཾ ཧེརོད྄ ཛྱོཏིཪྻིདྦྷིརཱཏྨཱནཾ པྲཝཉྩིཏཾ ཝིཛྙཱཡ བྷྲྀཤཾ ཙུཀོཔ; ཨཔརཾ ཛྱོཏིཪྻྭིདྦྷྱསྟེན ཝིནིཤྩིཏཾ ཡད྄ དིནཾ ཏདྡིནཱད྄ གཎཡིཏྭཱ དྭིཏཱིཡཝཏྶརཾ པྲཝིཥྚཱ ཡཱཝནྟོ བཱལཀཱ ཨསྨིན྄ བཻཏླེཧམྣགརེ ཏཏྶཱིམམདྷྱེ ཙཱསན྄, ལོཀཱན྄ པྲཧིཏྱ ཏཱན྄ སཪྻྭཱན྄ གྷཱཏཡཱམཱས།
17 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
ཨཏཿ ཨནེཀསྱ ཝིལཱཔསྱ ནིནཱད: ཀྲནྡནསྱ ཙ། ཤོཀེན ཀྲྀཏཤབྡཤྩ རཱམཱཡཱཾ སཾནིཤམྱཏེ། སྭབཱལགཎཧེཏོཪྻཻ རཱཧེལ྄ ནཱརཱི ཏུ རོདིནཱི། ན མནྱཏེ པྲབོདྷནྟུ ཡཏསྟེ ནཻཝ མནྟི ཧི༎
18 “An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
ཡདེཏད྄ ཝཙནཾ ཡིརཱིམིཡནཱམཀབྷཝིཥྱདྭཱདིནཱ ཀཐིཏཾ ཏཏ྄ ཏདཱནཱིཾ སཕལམ྄ ཨབྷཱུཏ྄།
19 Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
ཏདནནྟརཾ ཧེརེདི རཱཛནི མྲྀཏེ པརམེཤྭརསྱ དཱུཏོ མིསརྡེཤེ སྭཔྣེ དརྴནཾ དཏྟྭཱ ཡཱུཥཕེ ཀཐིཏཝཱན྄
20 ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
ཏྭམ྄ ཨུཏྠཱཡ ཤིཤུཾ ཏནྨཱཏརཉྩ གྲྀཧཱིཏྭཱ པུནརཔཱིསྲཱཡེལོ དེཤཾ ཡཱཧཱི, ཡེ ཛནཱཿ ཤིཤུཾ ནཱཤཡིཏུམ྄ ཨམྲྀགཡནྟ, ཏེ མྲྀཏཝནྟཿ།
21 Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
ཏདཱནཱིཾ ས ཨུཏྠཱཡ ཤིཤུཾ ཏནྨཱཏརཉྩ གྲྀཧླན྄ ཨིསྲཱཡེལྡེཤམ྄ ཨཱཛགཱམ།
22 Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
ཀིནྟུ ཡིཧཱུདཱིཡདེཤེ ཨརྑིལཱཡནཱམ རཱཛཀུམཱརོ ནིཛཔིཏུ རྷེརོདཿ པདཾ པྲཱཔྱ རཱཛཏྭཾ ཀརོཏཱིཏི ནིཤམྱ ཏཏ྄ སྠཱནཾ ཡཱཏུཾ ཤངྐིཏཝཱན྄, པཤྩཱཏ྄ སྭཔྣ ཨཱིཤྭརཱཏ྄ པྲབོདྷཾ པྲཱཔྱ གཱལཱིལྡེཤསྱ པྲདེཤཻཀཾ པྲསྠཱཡ ནཱསརནྣཱམ ནགརཾ གཏྭཱ ཏཏྲ ནྱུཥིཏཝཱན྄,
23 ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”
ཏེན ཏཾ ནཱསརཏཱིཡཾ ཀཐཡིཥྱནྟི, ཡདེཏདྭཱཀྱཾ བྷཝིཥྱདྭཱདིབྷིརུཀྟྟཾ ཏཏ྄ སཕལམབྷཝཏ྄།