< Mattiyu 2 >

1 Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
Jésus étant né à Bethléem, dans la Judée, aux jours du roi Hérode, des mages arrivèrent d'Orient à Jérusalem.
2 suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
«Où est, demandèrent-ils, le nouveau-né, roi des Juifs? Nous avons vu son étoile en Orient et nous sommes venus pour l'adorer.»
3 Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
En entendant de telles paroles, le roi Hérode fut troublé et, avec lui, toute la ville de Jérusalem;
4 Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
il convoqua tous les chefs des prêtres et scribes du peuple et s'informa d'eux où devait naître le Christ.
5 Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
Ils lui répondirent: «A Bethléem dans la Judée.» (Voici, en effet, ce qui a été écrit par le prophète:
6 “‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
«Et toi, Bethléem, terre de Juda, Tu n'es certainement pas le plus petit des chefs-lieux de Juda, Car de toi sortira un conducteur Qui paîtra mon peuple, Israël.»)
7 Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
Là dessus, Hérode fit appeler les mages en secret et s'informa auprès d'eux de l'époque où l'étoile avait paru.
8 Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
Puis il les envoya à Bethléem. «Allez, leur dit-il, prenez des informations exactes sur cet enfant et, quand vous l'aurez trouvé, faites-le moi savoir, pour que, moi aussi, j'aille l'adorer.»
9 Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
Sur ces paroles du roi, ils partirent; et l'étoile qu'ils avaient vue en Orient les précédait jusqu'à ce que, parvenue au-dessus du lieu où était l'enfant, elle s'arrêta.
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
A la vue de l'étoile, ils se réjouirent d'une grande joie.
11 Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
Ils entrèrent dans la maison, ils virent l'enfant avec Marie sa mère; et, se prosternant, ils l'adorèrent. Ensuite, ouvrant leurs trésors, ils lui offrirent en présent de l'or, de l'encens et de la myrrhe.
12 Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
Ayant été miraculeusement avertis en songe de ne pas revenir vers Hérode, ils regagnèrent leur pays par un autre chemin.
13 Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
Après leur départ, un ange du Seigneur apparut en songe à Joseph et lui dit: «Lève-toi! prends l'enfant et sa mère, et fuis en Égypte où tu resteras jusqu'à ce que je te reparle; car Hérode va rechercher l'enfant afin de le faire périr.»
14 Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
Cette nuit même, Joseph se leva, prit l'enfant et sa mère et partit pour l'Égypte.
15 inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
Il y resta jusqu'à la mort d'Hérode. (C'était afin que fût accompli ce que le Seigneur avait dit par le prophète en ces mots: «J'ai rappelé mon fils d'Égypte».)
16 Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
Quant à Hérode, se voyant joué par les mages, il se mit fort en colère, et envoya tuer tous les enfants de Bethléem et de ses environs âgés de deux ans et au-dessous suivant l'époque dont il s'était informé auprès des mages.
17 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
(C'est alors que fut accompli ce qui avait été dit par le prophète Jérémie en ces mots:
18 “An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
«Une voix a été entendue dans Rama, Des pleurs et de longs sanglots; C'est Rachel pleurant ses enfants, Et elle ne veut pas être consolée parce qu'ils ne sont plus.»)
19 Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
Quand Hérode fut mort, un ange du Seigneur apparut en songe à Joseph en Égypte
20 ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
et lui dit: «Lève-toi, prends l'enfant et sa mère et retourne dans le pays d'Israël; car ceux qui en voulaient à la vie de l'enfant sont morts.»
21 Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
Joseph se levant donc prit l'enfant et sa mère et rentra dans le pays d'Israël.
22 Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
Mais ayant appris qu'Archélaüs régnait en Judée à la place d'Hérode son père, il appréhenda d'y aller. Miraculeusement averti en songe, il partit pour la province de Galilée
23 ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”
et, y étant arrivé, il habita une ville appelée Nazareth. (C'était afin que fut accompli ce qui a été dit par les prophètes: Il sera appelé Nazaréen).

< Mattiyu 2 >