< Mattiyu 2 >

1 Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
Jesus was born in Bethlehem [town] in Judea [province] during the time [MTY] that King Herod [the Great ruled there. Some time] after Jesus was born, some men who studied the stars and who lived in a [country] east [of Judea] came to Jerusalem.
2 suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
They asked [people], “Where is the one who has been born [in order that he might be] the king of [you] Jews? [We believe that your new king] has been born, because we have seen the star [that we believe indicated that] he has been [born]. [We saw it while we were in our country] east [of here]. So we have come to worship him.”
3 Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
When King Herod heard [what those men were asking], he became worried [that someone else might be proclaimed] {[people might proclaim someone else]} [king of the Jews to replace him]. Many [of the people] of Jerusalem [MTY, HYP] [also] became worried [because they were afraid of what King Herod might do].
4 Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
Then Herod gathered together all the ruling priests and men who taught the people the [Jewish] laws and he asked them where [the prophets had predicted that] the Messiah was to be born.
5 Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
They said to him, “[He will be born] in Bethlehem, [here] in Judea [province], because it was written by the prophet [Micah] {the prophet [Micah] wrote} [long ago what God said]:
6 “‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
‘You [who live in] Bethlehem [APO], in Judea [province], your town is certainly very important [LIT], because a man from your [town] will become a ruler. He will guide my people [who live in] Israel.’”
7 Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
Then [King] Herod secretly summoned those men who studied the stars. He asked them exactly when the star [first] appeared. [By what they told him, he was able to know the approximate age of the baby].
8 Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
Then he [concealed what he really planned to do and] said to them, “Go to Bethlehem and inquire thoroughly [where] the infant is. When you have found him, [come back and] report to me so that I, myself, can go [there and] worship him, too.”
9 Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
After the men heard what the king [told them], they went [toward Bethlehem]. To their surprise, the star that they had seen while they were in the eastern [country] went ahead of them [again] until it stood above [the house] where the child was.
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
When they saw the star, they rejoiced greatly [and followed it].
11 Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
They [found] the house and entered it and saw the child and his mother, Mary. They bowed down and worshipped him. Then they opened their treasure [boxes] [MTY] and they gave gold, [costly] frankincense, and myrrh to him.
12 Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
[Because] God [knew that King Herod planned to kill Jesus], in a dream the men who studied the stars were warned {he warned the men who studied the stars} that they should not return to [King] Herod. So they returned to their country, [but instead of traveling back on the same road, they] went on a different road.
13 Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
After the men who studied the stars left [Bethlehem], an angel [from] the Lord appeared to Joseph in a dream. He said, “Get up, take the child and his mother, and flee to Egypt. Stay there until I tell you [(sg) that you should leave], because [King] Herod is about [to send soldiers] to look for the child so that they can kill him.”
14 Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
So Joseph got up, he took the child and his mother [that] night, and they fled to Egypt.
15 inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
They stayed there until [King] Herod died, [and then they left Egypt]. By doing that, it was {they} fulfilled what the prophet [Hosea] wrote, which had been said by the Lord {which the Lord had said}, I have told my son to come out of Egypt.
16 Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
[While King] Herod [was still living], because he realized that he had been tricked by the men who studied the stars {the men who studied the stars had tricked him}, he became furious. Then, [assuming that Jesus was still in Bethlehem or the surrounding regions], Herod sent [soldiers there] to kill all the boy babies two years old and younger. [Herod calculated how old the baby was], according to what the men who studied the stars told him [about when the star first appeared].
17 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
[Because Bethlehem and Ramah towns were in the area where the descendants of Jacob’s wife Rachel lived, when soldiers killed the infant boys], they fulfilled what Jeremiah the prophet wrote,
18 “An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
[Women] in Ramah were weeping and wailing loudly. [Women who were the descendants] of Rachel, [the ancestor of the women there] [SYN], were grieving for [what happened to] their children. [Even though people tried to comfort them], they would not be comforted {stop mourning}, because their children were dead.
19 Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
After Herod died [and while Joseph and his family were still in Egypt], an angel that the Lord [had sent] appeared to Joseph in Egypt in a dream.
20 ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
He said to Joseph, “Take the child and his mother and go back to Israel [to live], because the people who were looking for the child [in order to kill him] have died.”
21 Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
So Joseph took the child and his mother, and they went back to Israel.
22 Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
When Joseph heard that Archaelaus now ruled in Judea [district] instead of his father, [King] Herod [the Great], he was afraid to go there. Because he was warned {[God] warned Joseph} in a dream [that it was still dangerous for them to live in Judea], he [and Mary and Jesus] went to Galilee [District]
23 ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”
to Nazareth [to live there]. The result was that what had been said by the ancient prophets {what the ancient prophets had said} [about the Messiah], that he would be called {people would call him} a Nazareth-man, was fulfilled {came true}.

< Mattiyu 2 >