< Mattiyu 2 >

1 Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
Now after Jesus was born in Bethlehem of Judea, in the days of Herod the king, behold, wise men [magi] from the East came into Jerusalem,
2 suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
saying: “Where is he who has been born King of the Jews? For we saw his star in the East and have come to worship him.”
3 Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
When Herod the king heard it he became agitated, and all Jerusalem with him.
4 Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
And gathering all the chief priests and scribes of the people, he inquired of them where the Christ was to be born.
5 Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
So they said to him: “In Bethlehem of Judea, for thus it stands written by the prophet:
6 “‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
‘And you, Bethlehem, land of Judah, are not at all the least among the rulers of Judah, for out of you will come a Ruler who will shepherd my people Israel.’”
7 Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
Then Herod, calling the wise men secretly, determined from them the time when the star appeared.
8 Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
And directing them to Bethlehem he said, “When you get there, search carefully for the young child; and should you find him, bring back word to me, so that I also may go and worship him.”
9 Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
So having heard the king they departed, and there was the star that they had seen in the East! It went before them until it arrived and stopped above where the young Child was.
10 Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
Now when they saw the star they rejoiced with exceedingly great joy!
11 Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
And coming into the house they saw the young Child with Mary His mother, and falling down they worshiped Him; and opening their treasures they presented gifts to Him: gold, frankincense and myrrh.
12 Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
Then, having been warned in a dream not to return to Herod, they departed for their own country by a different road.
13 Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
Now when they had departed, again, an angel of the Lord appeared to Joseph in a dream saying: “Get up, take the young Child and His mother, flee to Egypt and stay there until I tell you; because Herod is about to seek the young Child to destroy Him!”
14 Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
So he got up and took the young Child and His mother by night and departed for Egypt.
15 inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
And he was there until the death of Herod, so that what was spoken by the Lord through the prophet should be fulfilled, namely: “Out of Egypt I called my Son.”
16 Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
Then Herod, when he saw that he had been deceived by the wise men, became very angry, and he sent out and killed all the boys who were in Bethlehem and in all its districts, from two years old and under, according to the time which he had determined from the wise men.
17 Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
Then what was spoken by Jeremiah the prophet was fulfilled, namely:
18 “An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
“A voice was heard in Ramah, lamentation, weeping and great mourning; Rachel weeping for her children and not wanting to be comforted, because they are no more.”
19 Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
Now Herod having died, there, an angel of the Lord appeared in a dream to Joseph in Egypt
20 ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
saying: “Get up, take the young Child and His mother and go into the land of Israel, for those seeking the life of the young Child have died.”
21 Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
So he got up and took the young Child and His mother and went into the land of Israel.
22 Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
But hearing that Archelaus was reigning over Judea instead of his father Herod, he was afraid to go there. And being warned in a dream he proceeded into the region of Galilee.
23 ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”
And upon arriving he settled in a city called Natsareth [Branch-town], so that what was spoken through the prophets should be fulfilled, that He would be called a Natsorean [Branch-man].

< Mattiyu 2 >