< Mattiyu 19 >
1 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
І сталось, як Ісус закінчи́в ці слова́, то Він ви́рушив із Галілеї, і прибув до країни Юдейської, на то́й бік Йорда́ну.
2 Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
А за Ним ішла бе́зліч наро́ду, — і Він уздоро́вив їх тут.
3 Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
І підійшли фарисеї до Нього, і, випробо́вуючи, запитали Його: „Чи дозволено дружи́ну свою відпускати з причини всякої?“
4 Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
А Він відповів і сказав: „Чи ви не читали, що Той, Хто створив споконві́ку людей, „створив їх чоловіком і жінкою?“
5 ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
І сказав: „Покине тому́ чоловік батька й матір, і пристане до дружи́ни своєї, — і стануть обо́є вони одним тілом“,
6 Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
тому́ то немає вже двох, але́ одне тіло. Тож, що Бог спарува́в, — людина нехай не розлу́чує!“
7 Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
Вони кажуть Йому: „А чому́ ж Мойсей заповів дати листа розводо́вого, та й відпускати?“
8 Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
Він говорить до них: „То за ваше жорстокосе́рдя дозволив Мойсей відпускати дружи́н ваших, споча́тку ж так не було́.
9 Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
А Я вам кажу́: Хто дружи́ну відпустить свою не з причини пере́любу, і одру́житься з іншою, той чинить пере́люб. І хто одру́житься з розве́деною, той чинить пере́люб“.
10 Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
Учні говорять Йому: „Коли справа така чоловіка із дружи́ною, то не добре одру́жуватись“.
11 Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
А Він їм відказав: „Це слово вміщають не всі, але ті, кому да́но.
12 Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
Бо бувають скопці, що з утро́би ще матерньої народилися так; є й скопці, що їх люди оскопи́ли, і є скопці, що самі оскопи́ли себе ради Царства Небесного. Хто може вмістити, — нехай вмістить“.
13 Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
Тоді привели Йому ді́ток, щоб поклав на них руки, і за них помолився, учні ж їм докоряли.
14 Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
Ісус же сказав: „Пустіть ді́ток, і не бороніть їм прихо́дити до Мене, — бо Царство Небесне належить таким“.
15 Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
І Він руки на них покла́в, та й пішов звідтіля́.
16 To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
І підійшов ось один, і до Нього сказав: „Учителю Добрий, що маю зробити я доброго, щоб мати життя вічне?“ (aiōnios )
17 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
Він же йому відказав: „Чого звеш Мене Добрим? Ніхто не є Добрий, крім Бога Само́го. Коли ж хочеш ввійти до життя, то виконай заповіді“.
18 Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
Той питає Його: „Які саме!“А Ісус відказав: „Не вбивай, не чини пере́любу, не кради́, не свідкуй неправдиво.
19 ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
Шануй батька та матір“, і: „Люби свого ближнього, як само́го себе“.
20 Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
Говорить до Нього юна́к: „Це я виконав все. Чого́ ще бракує мені?“
21 Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
Ісус каже йому: „Коли хочеш бути досконалим, — піди, продай до́бра свої та й убогим роздай, — і матимеш скарб ти на небі. Пото́му приходь та й іди вслід за Мною“.
22 Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
Почувши ж юна́к таке слово, відійшов, зажурившись, — бо великі маєтки він мав.
23 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
Ісус же сказав Своїм учням: Поправді кажу вам, що багатому трудно ввійти в Царство Небесне.
24 Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Іще вам кажу́: Верблю́дові легше пройти через го́лчине ву́шко, ніж багатому в Боже Царство ввійти́!“
25 Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
Як учні ж Його це зачули, здивувалися дуже й сказали: „Хто́ ж тоді може спасти́ся?“
26 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
А Ісус позирнув і сказав їм: „Неможливе це лю́дям, та можливе все Богові“.
27 Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
Тоді відізвався Петро та до Нього сказав: „От усе ми покинули, та й пішли за Тобою слідом; що́ ж нам буде за це?“
28 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
А Ісус відказав їм: „Поправді кажу́ вам, що коли, при відно́вленні світу, Син Лю́дський засяде на престолі слави Своєї, тоді сядете й ви, що за Мною пішли, на дванадцять престолів, щоб судити дванадцять племе́н Ізраїлевих.
29 Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
І кожен, хто за Йме́ння Моє кине дім, чи братів, чи сесте́р, або ба́тька, чи матір, чи діти, чи зе́млі, — той багатокротно одержить і успадку́є вічне життя. (aiōnios )
30 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.
І багато-хто з перших останніми стануть, а останні — першими.