< Mattiyu 19 >

1 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
Jésus ayant achevé ces discours, quitta la Galilée, et vint aux frontières de la Judée, au delà du Jourdain.
2 Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
Une grande multitude le suivit, et là il guérit les malades.
3 Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
Alors les Pharisiens l’abordèrent pour le tenter; ils lui dirent: « Est-il permis à un homme de répudier sa femme pour quelque motif que ce soit? »
4 Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
Il leur répondit: « N’avez-vous pas lu que le Créateur, au commencement, les fit homme et femme, et qu’il dit:
5 ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
À cause de cela, l’homme quittera son père et sa mère, et s’attachera à sa femme, et ils deviendront les deux une seule chair. —
6 Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
Ainsi ils ne sont plus deux, mais une seule chair. Que l’homme ne sépare donc pas ce que Dieu a uni. »
7 Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
« Pourquoi donc, lui dirent-ils, Moïse a-t-il prescrit de donner un acte de divorce et de renvoyer la femme? »
8 Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
Il leur répondit: « C’est à cause de la dureté de vos cœurs que Moïse vous a permis de répudier vos femmes: au commencement, il n’en fut pas ainsi.
9 Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
Mais je vous le dis, celui qui renvoie sa femme, si ce n’est pour impudicité, et en épouse une autre, commet un adultère; et celui qui épouse une femme renvoyée, se rend adultère. »
10 Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
Ses disciples lui dirent: « Si telle est la condition de l’homme à l’égard de la femme, il vaut mieux ne pas se marier. »
11 Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
Il leur dit: « Tous ne comprennent pas cette parole, mais seulement ceux à qui cela a été donné.
12 Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
Car il y a des eunuques qui le sont de naissance, dès le sein de leur mère; il y a aussi des eunuques qui le sont devenus par la main des hommes; et il y en a qui se sont faits eunuques eux-mêmes à cause du royaume des cieux. Que celui qui peut comprendre, comprenne! »
13 Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
Alors on lui présenta de petits enfants pour qu’il leur imposât les mains et priât pour eux. Et comme les disciples reprenaient ces gens,
14 Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
Jésus leur dit: « Laissez ces petits enfants, et ne les empêchez pas de venir à moi, car le royaume des cieux est pour ceux qui leur ressemblent. »
15 Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
Et, leur ayant imposé les mains, il continua sa route.
16 To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios g166)
Et voici qu’un jeune homme, l’abordant, lui dit: « Bon Maître, quel bien dois-je faire pour avoir la vie éternelle? » (aiōnios g166)
17 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
Jésus lui répondit: « Pourquoi m’appelles-tu bon? Dieu seul est bon. Que si tu veux entrer dans la vie, garde les commandements. » —
18 Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
« Lesquels? » dit-il. Jésus répondit: « Tu ne tueras point; tu ne commettras point d’adultère; tu ne déroberas point; tu ne rendras point de faux témoignage.
19 ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
Honore ton père et ta mère, et aime ton prochain comme toi-même. »
20 Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
Le jeune homme lui dit: « J’ai observé tous ces commandements depuis mon enfance; que me manque-t-il encore? »
21 Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
Jésus lui dit: « Si tu veux être parfait, va, vends ce que tu as, donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel; puis viens et suis-moi. »
22 Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
Lorsqu’il eut entendu ces paroles, le jeune homme s’en alla triste; car il avait de grands biens.
23 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
Et Jésus dit à ses disciples: « Je vous le dis en vérité, difficilement un riche entrera dans le royaume des cieux.
24 Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Je vous le dis encore une fois, il est plus aisé qu’un chameau passe par le trou d’une aiguille, qu’il ne l’est à un riche d’entrer dans le royaume des cieux. »
25 Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
En entendant ces paroles, les disciples étaient fort étonnés, et ils dirent: « Qui peut donc être sauvé? »
26 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
Jésus les regarda et leur dit: « Cela est impossible aux hommes; mais tout est possible à Dieu. »
27 Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
Alors Pierre, prenant la parole: « Voici, dit-il, que nous avons tout quitté pour vous suivre; qu’avons-nous donc à attendre? »
28 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
Jésus leur répondit: « Je vous le dis en vérité, lorsque, au jour du renouvellement, le Fils de l’homme sera assis sur le trône de sa gloire, vous qui m’avez suivi, vous siégerez aussi sur douze trônes, et vous jugerez les douze tribus d’Israël.
29 Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios g166)
Et quiconque aura quitté des maisons, ou des frères, ou des sœurs, ou un père, ou une mère, ou une femme, ou des enfants, ou des champs à cause de mon nom, il recevra le centuple et possédera la vie éternelle. » (aiōnios g166)
30 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.
« Et plusieurs qui sont les premiers seront les derniers, et plusieurs qui sont les derniers seront les premiers. »

< Mattiyu 19 >