< Mattiyu 19 >

1 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
When Jesus had finished these discourses, He removed from Galilee and came into that part of Judaea which lay beyond the Jordan.
2 Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
And a vast multitude followed him, and He cured them there.
3 Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
Then came some of the Pharisees to Him to put Him to the proof by the question, "Has a man a right to divorce his wife whenever he chooses?"
4 Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
"Have you not read," He replied, "that He who made them 'made them' from the beginning 'male and female,
5 ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
and said, For this reason a man shall leave his father and mother and be united to his wife, and the two shall be one'?
6 Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
Thus they are no longer two, but 'one'! What therefore God has joined together, let not man separate."
7 Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
"Why then," said they, "did Moses command the husband to give her 'a written notice of divorce,' and so put her away?"
8 Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
"Moses," He replied, "in consideration of the hardness of your nature permitted you to put away your wives, but it has not been so from the beginning.
9 Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
And I tell you that whoever divorces his wife for any reason except her unfaithfulness, and marries another woman, commits adultery."
10 Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
"If this is the case with a man in relation to his wife," said the disciples to Him, "it is better not to marry."
11 Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
"It is not every man," He replied, "who can receive this teaching, but only those on whom the grace has been bestowed.
12 Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
There are men who from their birth have been disabled from marriage, others who have been so disabled by men, and others who have disabled themselves for the sake of the Kingdom of the Heavens. He who is able to receive this, let him receive it."
13 Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
Then young children were brought to Him for Him to put His hands on them and pray; but the disciples interfered.
14 Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
Jesus however said, "Let the little children come to me, and do not hinder them; for it is to those who are childlike that the Kingdom of the Heavens belongs."
15 Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
So He laid His hands upon them and went away.
16 To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios g166)
"Teacher," said one man, coming up to Him, "what that is good shall I do in order to win the Life of the Ages?" (aiōnios g166)
17 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
"Why do you ask me," He replied, "about what is good? There is only One who is truly good. But if you desire to enter into Life, keep the Commandments."
18 Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
"Which Commandments?" he asked. Jesus answered, "'Thou shalt not kill;' 'Thou shalt not commit adultery;' 'Thou shalt not steal;' 'Thou shalt not lie in giving evidence;'
19 ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
'Honour thy father and thy mother'; and 'Thou shalt love thy fellow man as much as thyself.'"
20 Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
"All of these," said the young man, "I have carefully kept. What do I still lack?"
21 Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
"If you desire to be perfect," replied Jesus, "go and sell all that you have, and give to the poor, and you shall have wealth in Heaven; and come, follow me."
22 Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
On hearing those words the young man went away much cast down; for he had much property.
23 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
So Jesus said to His disciples, "I solemnly tell you that it is with difficulty that a rich man will enter the Kingdom of the Heavens.
24 Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Yes, I tell you, it is easier for a camel to go through the eye of a needle than for a rich man to enter the Kingdom of God."
25 Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
These words utterly amazed the disciples, and they asked, "Who then can be saved?"
26 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
Jesus looked at them and said, "With men this is impossible, but with God everything is possible."
27 Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
Then Peter said to Jesus, "See, we have forsaken everything and followed you; what then will be our reward?"
28 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
"I solemnly tell you," replied Jesus, "that in the New Creation, when the Son of Man has taken His seat on His glorious throne, all of you who have followed me shall also sit on twelve thrones and judge the twelve tribes of Israel.
29 Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios g166)
And whoever has forsaken houses, or brothers or sisters, or father or mother, or children or lands, for my sake, shall receive many times as much and shall have as his inheritance the Life of the Ages. (aiōnios g166)
30 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.
"But many who are now first will be last, and many who are now last will be first.

< Mattiyu 19 >