< Mattiyu 19 >
1 Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
Og det skete, da Jesus havde fuldendt disse Ord, drog han bort fra Galilæa og kom til Judæas Egne, hinsides Jordan.
2 Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
Og store Skarer fulgte ham, og han helbredte dem der.
3 Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
Og Farisæerne kom til ham, fristede ham og sagde: "Er det tilladt at skille sig fra sin Hustru af hvilken som helst Grund?"
4 Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
Men han svarede og sagde: "Have I ikke læst, at Skaberen fra Begyndelsen skabte dem som Mand og Kvinde
5 ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
og sagde: Derfor skal en Mand forlade sin Fader og sin Moder og holde sig til sin Hustru, og de to skulle blive til eet Kød?
6 Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
Således ere de ikke længer to, men eet Kød. Derfor, hvad Gud har sammenføjet, må et Menneske ikke adskille."
7 Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
De sige til ham: "Hvorfor bød da Moses at give et Skilsmissebrev og skille sig fra hende?"
8 Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
Han siger til dem: "Moses tilstedte eder at skille eder fra eders Hustruer for eders Hjerters Hårdheds Skyld; men fra Begyndelsen har det ikke været således.
9 Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
Men jeg siger eder, at den, som skiller sig fra sin Hustru, når det ikke er for Hors Skyld, og tager en anden til Ægte, han bedriver Hor; og den, som tager en fraskilt Hustru til Ægte, han bedriver Hor."
10 Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
Hans Disciple sige til ham: "Står Mandens Sag med Hustruen således, da er det ikke godt at gifte sig."
11 Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
Men han sagde til dem: "Ikke alle rummer dette Ord, men de, hvem det er givet:
12 Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
Thi der er Gildinger, som ere fødte således fra Moders Liv; og der er Gildinger, som ere gildede af Mennesker; og der er Gildinger, som have gildet sig selv for Himmeriges Riges Skyld. Den, som kan rumme det, han rumme det!"
13 Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
Da blev der båret små Børn til ham, for at han skulde lægge Hænderne på dem og bede; men Disciplene truede dem.
14 Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
Da sagde Jesus: "Lader de små Børn komme, og formener dem ikke at komme til mig; thi Himmeriges Rige hører sådanne til."
15 Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
Og han lagde Hænderne på dem, og han drog derfra.
16 To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
Og se, en kom til ham og sagde: "Mester! hvad godt skal jeg gøre, for at jeg kan få et evigt Liv?" (aiōnios )
17 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
Men han sagde til ham: "Hvorfor spørger du mig om det gode? Een er den gode. Men vil du indgå til Livet, da hold Budene!"
18 Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
Han siger til ham: "Hvilke?" Men Jesus sagde: "Dette: Du må ikke slå ihjel; du må ikke bedrive Hor; du må ikke stjæle; du må ikke sige falsk Vidnesbyrd;
19 ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
ær din Fader og din Moder, og: Du skal elske din Næste som dig selv."
20 Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
Den unge Mand siger til ham: "Det har jeg holdt alt sammen; hvad fattes mig endnu?"
21 Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
Jesus sagde til ham: "Vil du være fuldkommen, da gå bort, sælg, hvad du ejer, og giv det til fattige, så skal du have en Skat i Himmelen; og kom så og følg mig!"
22 Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
Men da den unge Mand hørte det Ord, gik han bedrøvet bort; thi han havde meget Gods.
23 Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
Men Jesus sagde til sine Disciple: "Sandelig, siger jeg eder: En rig Kommer vanskeligt ind i Himmeriges Rige.
24 Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Atter siger jeg eder: Det er lettere for en Kamel at gå igennem et Nåleøje end for en rig at gå ind i Guds Rige."
25 Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
Men da Disciplene hørte dette, forfærdedes de såre og sagde: "Hvem kan da blive frelst?"
26 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
Men Jesus så på dem og sagde: "For Mennesker er dette umuligt, men for Gud ere alle Ting mulige."
27 Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
Da svarede Peter og sagde til ham: "Se, vi have forladt alle Ting og fulgt dig; hvad skulle da vi have?"
28 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
Men Jesus sagde til dem: "Sandelig, siger jeg eder, at i Igenfødelsen, når Menneskesønnen sidder på sin Herligheds Trone, skulle også I, som have fulgt mig, sidde på tolv Troner og dømme Israels tolv Stammer.
29 Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
Og hver, som har forladt Hus eller Brødre eller Søstre eller Fader eller Moder eller Hustru eller Børn eller Marker for mit Navns Skyld, skal få det mange Fold igen og arve et evigt Liv. (aiōnios )
30 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.
Men mange af de første skulle blive de sidste, og af de sidste de første.