< Mattiyu 18 >

1 A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
V tem času pristopijo učenci k Jezusu, govoreč: Kdo je torej v nebeškem kraljestvu največi?
2 Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
In Jezus pokliče otroka in ga postavi sred njih,
3 Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
In reče: Resnično vam pravim, če se ne spreobrnete in ne postanete kakor otroci, ne boste prišli v nebeško kraljestvo.
4 Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
Kdor se torej poniža kakor ta otrok, ta bo v nebeškem kraljestvu največi.
5 Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
In kdorkoli sprejme enega takošnega otroka v ime moje, sprejema mene.
6 “Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
Kdor pa pohujša enega teh malih, ki verujejo v mé, bilo bi mu bolje, da bi mu se obesil mlinsk kamen na vrat, in bi se utopil v morskej globočini.
7 Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
Gorjé svetu za voljo pohujšanja! Pohujšanje sicer mora priti; ali gorjé tistemu človeku, po kterem pohujšanje pride.
8 In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
Če te pa roka tvoja ali noga tvoja pohujšuje, odseci ji, in vrzi od sebe; bolje ti je hromemu ali brez roke priti v življenje, nego dve roki in dve nogi imeti, in vrženemu biti v večni ogenj. (aiōnios g166)
9 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
In če te pohujšuje oko tvoje, izderi ga, in vrzi od sebe; bolje ti je z enim očesom priti v življenje, nego dve očesi imeti, in vrženemu biti v peklenski ogenj. (Geenna g1067)
10 “Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
Glejte, da ne boste prezirali enega teh malih; kajti resnično vam pravim, da gledajo njih angelji na nebesih vsakedaj obličje očeta mojega, ki je na nebesih.
Kajti sin človečji je prišel, da zveliča, kar se je izgubilo.
12 “Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
Kaj se vam zdí? Če ima en človek sto ovâc, in ena od njih zajde: ne popustí li devet in devetdeseterih, pa gre na gore, in išče tiste, ki je zašla?
13 In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
In če se zgodi, da jo najde, resnično vam pravim, da se nad njo bolj veselí, nego nad devet in devetdeseterimi, ktere niso zašle.
14 Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
Tako ni volja očeta vašega, ki je na nebesih, da bi poginil eden od teh malih.
15 “In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
Če se pa pregreší brat tvoj zoper tebe, pojdi, in ograjaj ga med seboj in njim samim; če te posluša, pridobil si brata svojega.
16 Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
Če pa ne posluša, vzemi seboj še enega ali dva, da ostane vsaka beseda v ustih dveh ali treh prič.
17 In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
Če jih pa ne posluša, povej cerkvi; če pa tudi cerkve ne posluša, naj ti bo ko pogan in mitar.
18 “Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
Resnično vam pravim: Karkoli zvežete na zemlji, zvezano bo na nebesih; in karkoli razvežete na zemlji, razvezano bo na nebesih.
19 “Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
Zopet vam pravim, da če se dva od vas zedinita na zemlji o čemerkoli, kar prosita, zgodilo jima se bo od očeta mojega, ki je na nebesih.
20 Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
Kajti, kjer sta dva ali trije zbrani v ime moje, tam sem jaz sredi njih.
21 Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
Tedaj pristopi k njemu Peter in reče: Gospod! kolikokrat se bo pregrešil brat moj zoper mene in mu bom odpustil? do sedemkrat?
22 Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
Jezus mu reče: Ne pravim ti, do sedemkrat, nego do sedemdesetkrat sedemkrat.
23 “Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
Za to je nebeško kraljestvo podobno človeku kralju, kteri je hotel s hlapci svojimi račun napraviti.
24 Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
In ko je jel računiti, pripeljejo mu enega, kteri je bil dolžen tisoč talentov.
25 Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
Ker pa ni imel, da bi plačal, ukaže gospodar njegov prodati njega, in ženo njegovo in otroke, in vse, kar je imel, in naj mu se plača.
26 “Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
Hlapec pa pade, ter mu se je poklanjal, govoreč: Gospod! potrpi me, in vse ti bom plačal.
27 Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
Gospodarju se pa ta hlapec zasmili: in prizanese mu, in dolg mu odpustí.
28 “Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
Ko pa ta hlapec izide, najde enega svojih tovarišev, kteri mu je bil sto grošev dolžen; in zgrabivši ga, davil ga je, govoreč: Plačaj mi, kar si dolžen!
29 “Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
Tovariš njegov pa pade k nogam njegovim, ter ga je prosil, govoreč: Potrpi me, in vse ti bom plačal.
30 “Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
On pa ni hotel; nego odide in ga vrže v ječo, dokler ne plača dolga.
31 Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
Videvši pa tovariši njegovi, kar se je zgodilo, užali jim se zeló; ter pridejo in povedó gospodarju svojemu vse, kar se je zgodilo.
32 “Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
Tedaj ga gospodar njegov pokliče in mu reče: Hudobni hlapec! odpustil sem ti ves tisti dolg, ker si me prosil.
33 Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
Ali se nisi imel tudi ti tovariša svojega usmiliti, kakor sem se tudi jaz tebe usmilil?
34 Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
In gospodar njegov se ujezí in ga izročí trinogom, dokler ne poplača vsega, kar mu je bil dolžen.
35 “Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”
Tako bo storil tudi oče moj nebeški vam, če ne odpustite vsak bratu svojemu iz srca svojega njih pregreh.

< Mattiyu 18 >