< Mattiyu 18 >

1 A lokacin nan sai almajirai suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Wane ne mafi girma a mulkin sama?”
At that hour the disciples came to Jesus, and said: Who then is greatest in the kingdom of heaven?
2 Sai ya kira ƙaramin yaro ya sa shi yă tsaya a tsakiyarsu.
And Jesus called a little child to him, and placed him in the midst of them,
3 Sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in ba kun canja kuka zama kamar ƙananan yara ba, labudda, ba za ku shiga mulkin sama ba.
and said: Verily I say to you, Unless you turn and become as little children, you can not enter the kingdom of heaven.
4 Saboda haka, duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar wannan yaro, shi ne mafi girma a mulkin sama.
Whoever, therefore, humbles himself as this little child, is greatest in the kingdom of heaven.
5 Duk kuma wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan a cikin sunana ya karɓe ni ne.
And whoever receives one such little child on my account, receives me;
6 “Amma duk wanda ya sa ɗaya daga cikin ƙananan nan da suka gaskata da ni ya yi zunubi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.
but whoever ensnares one of these little ones that believe in me, it were better for him that a millstone were hung about his neck, and that he were drowned in the depth of the sea.
7 Kaiton duniya saboda abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi! Dole irin waɗannan abubuwa su zo, sai dai kaiton mutumin da ya zama sanadin kawo su!
Alas for the world because of snares! for it is necessary that snares come: but alas for that man by whom the snare comes!
8 In hannunka ko ƙafarka yana sa ka zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da hannu ko ƙafa ɗaya da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu da a jefar da kai cikin madawwamiyar wuta da hannuwa biyu ko ƙafafu biyu. (aiōnios g166)
If, then, your hand or your foot ensnares you, cut it off, and throw it from you. It is better for you to enter into life lame or maimed, than, having two hands or two feet, to be thrown into the eternal fire. (aiōnios g166)
9 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta da idanunka biyu. (Geenna g1067)
And if your eye ensnares you, pull it out, and throw it from you. It is better to enter into life with one eye, than, having two eyes, to be thrown into hell-fire. (Geenna g1067)
10 “Ku lura, kada ku rena ɗaya daga cikin waɗannan ƙanana. Gama ina faɗa muku mala’ikunsu a sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin sama.
Take heed that you despise not one of these little ones: for I say to you, That their angels in heaven do always behold the face of my Father who is in heaven.
For the Son of man has come to save that which is lost.
12 “Me kuka gani? In wani yana da tumaki ɗari, sai ɗaya daga cikinsu ta ɓace, ba sai yă bar tasa’in da taran a kan tuddai yă je neman guda ɗayan da ta ɓace ba?
What think you? If a man have a hundred sheep, and one of them go astray, does he not leave the ninety-nine, and go into the mountains, and seek for that which has gone astray?
13 In kuwa ya same ta, ina gaya muku gaskiya, zai yi murna saboda ɗayan fiye da tasa’in da taran da ba su ɓace ba.
And if it so be that he find it, verily I say to you, he rejoices over it more than over the ninety-nine that did not go astray.
14 Haka ma Ubanku da yake cikin sama ba ya so ko ɗaya daga cikin ƙananan nan yă ɓace.
Even so, it is not the will of your Father who is in heaven, that one of these little ones should be lost.
15 “In ɗan’uwanka ya yi maka laifi, ka je ka nuna masa laifinsa, tsakaninku biyu kaɗai. In ya saurare ka, ka maido da ɗan’uwanka ke nan.
And if your brother sin against you, go and tell him of his fault between you and him alone; if he hear you, you have gained your brother.
16 Amma in bai saurare ka ba, ka je tare da mutum ɗaya ko biyu, domin ‘a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku.’
But if he will not hear you, take with you one or two more, that, by the mouth of two or three witnesses, every word may be established.
17 In kuwa ya ƙi yă saurare su, sai ka gaya wa ikkilisiya; in kuma ya ƙi yă saurari ikkilisiya ma, ka yi da shi kamar marar sanin Allah ko mai karɓar haraji.
But if he refuse to hear them, tell it to the church; and if he also refuse to hear the church, let him be to you as a heathen man and a publican.
18 “Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka daure a duniya, za a daure a sama, duk kuma abin da kuka kunce a duniya, za a kunce shi a sama.
Verily, I say to you, my disciples, Whatever you bind on earth, shall be bound in heaven; and whatever you loose on earth, shall be loosed in heaven.
19 “Har wa yau, ina gaya muku cewa in mutum biyu a cikinku a duniya suka yarda su roƙi wani abu, Ubana da yake cikin sama zai yi muku.
Again, I say to you, that if two of you agree on earth about any thing for which they will ask, it shall be done for them by my Father who is in heaven.
20 Gama inda mutum biyu ko uku suka taru cikin sunana, a can ma ina tare da su.”
For where there are two or three that have come together for my sake, there I am in the midst of them.
21 Sai Bitrus ya zo wurin Yesu ya yi masa tambaya ya ce, “Ubangiji, sau nawa zan yafe wa ɗan’uwana sa’ad da ya yi mini zunubi? Har sau bakwai?”
Then Peter came to him, and said: Lord, how often shall my brother sin against me, and I forgive him? Till seven times?
22 Yesu amsa ya ce, “Ina gaya maka, ba sau bakwai ba, amma sau saba’in da bakwai.
Jesus said to him: I say to you, Not till seven times, but till seventy times seven.
23 “Saboda haka, mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya so yă yi ƙididdigar dukiyarsa da take a hannun bayinsa.
For this reason, the kingdom of heaven is likened to a king that wished to settle accounts with his servants.
24 Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wani wanda yake bin bashin talenti dubu goma.
And when he began to make a settlement, there was brought to him one that owed him ten thou sand talents.
25 Da yake bai iya biya ba, sai maigida ya umarta a sayar da shi da matarsa da yaransa da kuma duk abin da yake da shi, a biya bashin.
But as he was not able to pay, his lord commanded him, and his wife, and children, and all that he had, to be sold, and payment to be made.
26 “Bawan ya durƙusa a gabansa. Ya yi roƙo ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka ƙaf.’
Therefore, the servant fell down and besought him, saying, Have patience with me, Lord, and I will pay you all.
27 Maigidan bawan ya ji tausayinsa, ya yafe masa bashin, ya kuma sake shi.
And the lord of that servant was moved with compassion, and let him go, and forgave him the debt.
28 “Amma da wannan bawa ya fita, sai ya gamu da wani abokin bautarsa wanda yake binsa bashin dinari ɗari. Sai ya cafke shi, ya shaƙe shi a wuya yana cewa, ‘Biya ni abin da nake binka!’
But that servant went out, and found one of his fellow-servants, who owed him a hundred denarii; and he laid hold of him, and took him by the throat, saying: Pay me what you owe.
29 “Wannan abokin bautarsa ya durƙusa ya roƙe shi, ‘Ka yi mini haƙuri, zan biya ka.’
Then his fellow-servant fell down at his feet, and besought him, saying: Have patience with me, and I will pay you all.
30 “Amma ya ƙi. A maimako, sai ya je ya sa aka jefa shi a kurkuku, har yă biya bashin.
And he would not; but went and threw him into prison, till he should pay the debt.
31 Sa’ad da sauran bayin suka ga abin da ya faru, abin ya ɓata musu rai ƙwarai, sai suka tafi suka faɗa wa maigidansu dukan abin da ya faru.
When his fellow-servants saw what was done, they were very sad, and went and made known to their lord all that was done.
32 “Sai maigidan ya kira wannan bawa. Ya ce, ‘Kai mugun bawa, na yafe duk bashin da nake binka domin ka roƙe ni.
Then his lord called him and said to him: Wicked servant! I forgave you all that debt, because you besought me.
33 Ashe, bai kamata kai ma ka ji tausayin abokin bautarka yadda na yi maka ba?’
Ought you not to have had mercy on your fellow-servant, even as I had mercy on you?
34 Cikin fushi, maigidan ya miƙa shi ga ma’aikatan kurkuku su gwada masa azaba, har yă biya dukan bashin da ake binsa.
And his lord was angry, and delivered him to the jailers, till he should pay all that was due him.
35 “Haka Ubana da yake cikin sama zai yi da kowannenku, in ba ku yafe wa’yan’uwanku daga zuciyarku ba.”
So also will my heavenly Father do to you, if, from your hearts, you forgive not every one his brother’s offenses.

< Mattiyu 18 >